Dubi wasu jahohi guda 12 a Najeriya da ba’a samu bullar cutar COVID-19 ba

Dubi wasu jahohi guda 12 a Najeriya da ba’a samu bullar cutar COVID-19 ba

Duk da yadda annobar Coronavirus ke cigaba da yaduwa a Najeriya kamar wutar kara, akwai wasu jahohi guda goma sha biyu da har yanzu ba’a samu bullar cutar a cikinsu ba.

Jaridar Punch ta ruwaito zuwa yanzu cutar Coronavirus ta shiga jahohi 25 da kuma babban birnin tarayya Abuja, inda ta kama mutane 782, ta kashe 25.

KU KARANTA: Sojoji sun yi ma yan bindiga ruwan bamabamai a wani kauyen Neja

Wadannan jahohi da cutar bata ratsa su ba sun hada da: Adamawa, Bayelsa, Cross River, Ebonyi, Imo, Kebbi, Kogi, Nasarawa, Plateau, Taraba, Yobe da kuma jahar Zamfara

Sai dai duk da haka gwamnatocin jahohin basu yi kasa a gwiwa ba, suna cigaba da daukan matakan kandagarki domin kuwa annobar babu ruwanta da jaha ko jam’iyya.

Dubi wasu jahohi guda 12 a Najeriya da ba’a samu bullar cutar COVID-19 ba
Dubi wasu jahohi guda 12 a Najeriya da ba’a samu bullar cutar COVID-19 ba
Asali: UGC

A yanzu gwamnonin jahar Plateau, Nassarawa, Yobe da Imo sun garkame iyakokin jahohinsu babu shiga babu fita, wannan wani mataki ne na kare baki daga shigar musu da cutar.

A hannu guda kuma, hukumar kare yaduwar cututtuka a Najeriya, NCDC ta sanar da samun karuwar sabbin mutane 117 da suka kamu da cutar Coronavirus a Najeriya.

“Zuwa karfe 11:25 na daren Talata, 21 ga watan Afrilu, akwai mutane 782 da aka tabbatar suna dauke da cutar COVID-19 da aka samu rahotonsu a Najeriya, 25 sun mutu, yayin da an sallami 197.” Inji NCDC.

Jahohin da aka samu sabbin mutanen da suka kamu da cutar sun hada da jahar Legas – 59, Kano 29, Borno 6, Katsina 4, Ogun 3, Rivers 1, da jahar Bauchi 1.

Ga jerin jahohin da cutar ta shiga da adadin mutanen da ta kama kamar haka; Legas-430, Abuja – 118, Kano- 73, Osun- 20, Edo- 15, Oyo- 16, Ogun- 20, Katsina- 16, Bauchi- 8, Kaduna- 9.

Sai kuma Akwa Ibom- 9 da Kwara-9, Borno-9, Delta- 4, Ondo- 3, Enugu- 2, Ekiti- 4, Rivers-3, Ondo- 3, Niger – 2, Benue- 1, Jigawa – 2, Gombe – 5, Sokoto – 1, Abia – 2, sai jahar Anambra- 1.

Ku biyo mu a https://facebook.com/legitnghausa

ko a http://twitter.com/legitnghausa

KU LATSA: Hanyar sauko da sabuwar manhajar jaridar Legit.com Hausa cikin sauki

Ga masu shawara ko korafi, a same mu a labaranhausa@corp.legit.com

Sanarwa na musamman: Shafin NAIJ Hausa ya koma Legit Hausa

Asali: Legit.ng

Authors:
Mudathir Ishaq avatar

Mudathir Ishaq Mudathir Ishaq is the head of the Hausa desk at Legit.ng. He studied Industrial Chemistry as first degree at the University of Abuja, Journalism (CSR Specialization) with the Michigan State University and runs MSc Industrial Chemistry from the Nasarawa State University, Keffi. With more than a decade experience in news reporting and content editing, he has interviewed influential personalities. He can be reached on: mudathir.ishaq@corp.legit.ng