‘Yan sanda sun kama wani fitinanne mai kisan mutane a jihar Rivers (Hotuna)
A ranar Alhamis 19 ga watan Satumba, 2019 ne rundunar ‘yan sandan Najeriya ta samu nasarar damke kasurgumin mai kisan mutanen nan, Gracious David a jihar Rivers.
David mai shekaru 26 ya shiga hannun ‘yan sanda ne a kan hanyarsa ta zuwa Uyo. David daya ne daga cikin ‘yan kungiyar shan jini ta Degbam. Kuma daga lokacin da aka kama shi zuwa yanzu rundunar ‘yan sandan ta ce ya sanar da ita bayanai masu matukar amfani.
KU KARANTA:Abinda ya sa muke neman sulhu da ‘yan bindiga, inji Sufeto janar na ‘yan sanda

Asali: Twitter
Majiyar ‘yan sandan ta sanar da mu cewa an cigaba da bincike akan wannan mutum domin gano ire-iren ayyukan da yake shirin aikata gabanin a kama shi.

Asali: Twitter
Mustapha Dandaura, Kwamishinan ‘yan sandan jihar zai zanta da manema labarai a ranar Juma’a 20 ga watan Satumba, 2019 game da kamen wannan mutum.
Ku biyo mu a https://facebook.com/legitnghausa
ko a http://twitter.com/legitcomhausa
KU LATSA: Hanyar sauko da sabuwar manhajar jaridar Legit.com Hausa cikin sauki
Ga masu shawara ko korafi, a same mu a labaranhausa@corp.legit.com
Sanarwa na musamman: Shafin NAIJ Hausa ya koma Legit Hausa
Asali: Legit.ng