Bayan samun nasara a rumfar zabe, mun sake yin nasara a kotu Allah abin godiya, inji Sanata Abbo

Bayan samun nasara a rumfar zabe, mun sake yin nasara a kotu Allah abin godiya, inji Sanata Abbo

Kotun sauraron zaben majalisar dokokin tarayya dake zaune a Jihar Adamawa ya bayyana Sanata Elisha Cliff Abbo a matsayin wanda sahihin wanda lashe zaben dan majalisar dattawa mai wakiltar Adamawa ta Arewa a zaben da ya gabata.

Sanata Binta Masi Garba ta jam’iyyar APC ce wadda ta kalubalanci zaben na Abbo. Binta ita ce tsohuwar sanatar da ta wakilci yankin a majalisa ta 8.

KU KARANTA:Boko Haram: Gwamnan Yobe ya bayyana fushinsa a kan harin da aka kai maihaifarsa kwanan nan

Kotun zaben ta yanke wannan hukuncin ne a ranar Alhamis 29 ga watan Agusta, inda ta yi watsi da karofin da aka shigar a kan zaben Sanata Abbo daga bisani kuma ta tabbatar da shi a matsayin wanda ya lashe zaben kamar yadda hukumar zabe ta INEC ta sanar a baya.

A wani dan takaitaccen bayani da ya wallafa a shafunkan sada zumunta dangane da wannan nasara, Abbo ya ce: “Ina taya al’ummar Madagali, Michika, Mubi ta arewa, Mubi ta kudu da Maiha murna. Munyi nasara a rumfar zabe ga shi kuma mun sake yin wata a kotu, Allah ne abin godiya.”

A ranar Litinin 29 ga watan Yuli, Sanata Abbo ya bada labarin yadda Rauf Aregbesola ya taba ba shi albashinsa na wata guda domin ya tsaya takarar shugabancin karamar hukumarsa a shekarar 2012.

Rauf Aregbesola, tsohon gwamnan Jihar Osun shi ne ministan tsaron cikin gidan Najeriya a yanzu.

Ku biyo mu a https://facebook.com/legitnghausa

ko a http://twitter.com/legitcomhausa

KU LATSA: Hanyar sauko da sabuwar manhajar jaridar Legit.com Hausa cikin sauki

Ga masu shawara ko korafi, a same mu a labaranhausa@corp.legit.com

Sanarwa na musamman: Shafin NAIJ Hausa ya koma Legit Hausa

Asali: Legit.ng

Authors:
Mudathir Ishaq avatar

Mudathir Ishaq Mudathir Ishaq is the head of the Hausa desk at Legit.ng. He studied Industrial Chemistry as first degree at the University of Abuja, Journalism (CSR Specialization) with the Michigan State University and runs MSc Industrial Chemistry from the Nasarawa State University, Keffi. With more than a decade experience in news reporting and content editing, he has interviewed influential personalities. He can be reached on: mudathir.ishaq@corp.legit.ng