A sanar damu wurin da aka kai Dadiyata, sakon matasan PDP zuwa ga Buhari

A sanar damu wurin da aka kai Dadiyata, sakon matasan PDP zuwa ga Buhari

-Kungiyar matasan PDP sun gudanar da zanga-zanga a Abuja a kan Abubakar Idris da aka yi gaba da shi tun ranar 8 ga wata

-Kungiyar ta nemi gwamnati ta yi mata bayanin wurin da aka kai wannan matashin wanda aka fi sani da suna Dadiyata

Kungiyar matasan jam’iyyar PDP a ranar Alhamis 15 ga watan Agusta sun roki Shugaba Buhari a kan a sanar da su inda aka kai Abubakar Idris wanda aka fi sani da Abu Hanifa Dadiyata.

Ana zargin jami’an tsaron DSS ne su kayi gaba da shi ranar Juma’a 8 ga watan Agusta zuwa wani wurin da ba a san ko ina bane.

KU KARANTA:Jerin sunayen sabbin kwamishinonin Jihar Oyo 14 da ma’aikatunsu

Kungiyar matasan ta bayyana Dadiyata a matsayin daya daga cikin wadanda ke yawan magana game da lamuran gwamnatin Najeriya.

Matasan wadanda suka shirya wata zanga-zanga a gaban Unity Fountain otel dake Abuja, sun bayyana cewa ko dai hukumar DSS ta sako dan uwansu ko kuma a kai shi gaban kotu.

Dauke a hannun matasan kwalaye inda suka rubuta ‘Ina Dadiyata’. A cewar kungiyar matasan wannan abinda da hukumar DSS tayi ya saba doka saboda an tsare shi sama da kwana biyu.

Matashin wanda yayi fice kwarai da gaske a shafukan sada zumunta wurin bayyana ra’ayinsa dangane da siyasar Najeriya, an nemi shi an rasa tun ranar 8 ga watan Agusta.

Bugu da kari, Abubakar Idris malami ne a Jami’ar gwamnatin tarayya dake Dutsenma cikin Jihar Katsina. Tun daga ranar Juma’a 8 ga wata har yanzu babu labarin wurin da Dadiyata yake.

Asali: Legit.ng

Authors:
Mudathir Ishaq avatar

Mudathir Ishaq Mudathir Ishaq is the head of the Hausa desk at Legit.ng. He studied Industrial Chemistry as first degree at the University of Abuja, Journalism (CSR Specialization) with the Michigan State University and runs MSc Industrial Chemistry from the Nasarawa State University, Keffi. With more than a decade experience in news reporting and content editing, he has interviewed influential personalities. He can be reached on: mudathir.ishaq@corp.legit.ng