Cin-hanci da rasahwa ne ke haifar mana da matsalolin tsaro, inji Magu

Cin-hanci da rasahwa ne ke haifar mana da matsalolin tsaro, inji Magu

-Ibrahim Magu ya fadi abinda ke haddasa karuwar rashin tsaro a kasar nan

-Shugaban hukumar ta EFCC ya ce cin-hanci da rashawa ne musabbabin aukuwar matsalolin tsaron Najeriya a hira da wani gidan rediyon Ibadan

-Magu ya samu wakilicin shugaban hukumar EFCC na Ibadan a lokacin shirin da aka yi ranara Talata

Mukaddashin Shugaban Hukumar yaki da cin-hanci da kuma yiwa tattalin arziki zagon kasa ta EFCC, Ibrahim Magu ya daura laifin tabarbarewar tsaron kasar nan kan cin-hanci da rashawa.

Magu yayi wannan bayanin ne a wata hira da ya yi da gidan rediyon Ibadan mai suna Diamond 101.1 FM a cikin shirinsu mai suna Eagle Alert ranar Talata.

KU KARANTA:Shi’a: Haramta IMN tamkar take musu hakkin yin addini ne, inji HRW

Magu wanda Shugaban hukumar EFCC na Ibadan, Friday Ebelo ya wakilta a lokacin da ake shirin ya ce, cin-hanci da rashawa ya bude kofar aikata muggan laifuka bila-adadin a kasar nan.

Ebelo ya ce: “ Ba zaka iya bambance lalacewar tsaro da cin-hanci da rashawa ba a kasar nan. Hanya daya tilo wadda zamu bi domin ceto kasar mu daga cikin wannan hali ita ce mu kawar da rashawa, sai kasarmu ta zauna lafiya.

“ Idan mu kayi nasarar dakile cin-hanci a kasar nan, zamu samu abubuwa da dama cikin sauki ta yadda za a samu yin manya-manyan ayyukan gina kasa cikin sauki, tare da samar da aikin yi ga marasa aiki musamman matasa a kasar nan.

“ Dole sai iyayen yara sun bada hadin kai wurin tarbiyar diyansu, ta hanyar tura yaran nasu makaranta domin neman ilimi, wannan ma abu ne wanda zai matukar taimakawa wannan kuduri.” A cewar Ebelo.

Ku biyo mu a https://facebook.com/legitnghausa

ko a http://twitter.com/legitcomhausa

KU LATSA: Hanyar sauko da sabuwar manhajar jaridar Legit.com Hausa cikin sauki

Ga masu shawara ko korafi, a same mu a labaranhausa@corp.legit.com

Sanarwa na musamman: Shafin NAIJ Hausa ya koma Legit Hausa

Asali: Legit.ng

Authors:
Mudathir Ishaq avatar

Mudathir Ishaq Mudathir Ishaq is the head of the Hausa desk at Legit.ng. He studied Industrial Chemistry as first degree at the University of Abuja, Journalism (CSR Specialization) with the Michigan State University and runs MSc Industrial Chemistry from the Nasarawa State University, Keffi. With more than a decade experience in news reporting and content editing, he has interviewed influential personalities. He can be reached on: mudathir.ishaq@corp.legit.ng