Majalisar dattawa taci alwashin dakatar da kamfanin Bet9ja
-Kwamitin matasa da wasanni na majalisar dattawa ya lashi takobin rufe kamfanin caca na Bet9ja idan har yaki amsa gayyatarsu
-Kwamitin ya riga da ya aikawa kamfanin goron gayyata a karo na farko inda kwamitin ke cewa rashin amsa gayyatar a karo na biyu zai haddasa hukunci mai tsauri
Kwamitin matasa da wasanni na majalisar dattawa yaci alwashin rufe kamfanin Bet9ja idan har kamfanin ya ki bayyana a gaban kwamitin a karo na biyu.
Shugaban wannan kwamiti, Obinna Ogba yayi wannan furuci lokacin da suke tantance kamfanonin buga caca dake aiki a Najeriya.
KU KARANTA:Bankwana da mulki: Saraki ya bukaci hadimansa su rubuta takardar ajiye aiki
Yace rashin halartar kamfanin zuwa wurin tantancewa abu da ya bamu mamaki saboda ko kadan basuyi tsammanin hakan ba.
Yayinda ya bukaci hadiminsa day a sake aikawa kamfanin da wata gayyata, sanatan ya fadi cewa “ Idan har suka ki amsa gayyatarmu a wannan karo tabbas zamu rufe kamfaninsu.”
Ya kara da cewa an shirya wannan taron tantancewa ne biyo bayan korafe-korafe daga bakin kamfanonin cacar kasar nan.
Wasu daga cikin masu wannan sana’a basu da ofishi idan kuma wasu sun kasance suna yin wannan sana’a ba tareda biyan gwamnati hakkinta ba.
Kimanin kamfanoni guda 20 suka bayyana gaban kwamitin a ranar Talata.
Ku biyo mu a https://facebook.com/legitnghausa
ko a http://twitter.com/legitcomhausa
KU LATSA: Hanyar sauko da sabuwar manhajar jaridar Legit.com Hausa cikin sauki
Ga masu shawara ko korafi, a same mu a labaranhausa@corp.legit.com
Sanarwa na musamman: Shafin NAIJ Hausa ya koma Legit Hausa
KU LATSA : Domin karuwa cikin wannan wata mai albarka na Ramadan
Asali: Legit.ng