Ahmed Aliyu da APC na neman kotun sauraren korefe korefen zabe ta janye damar da ta baiwa Tambuwal

Ahmed Aliyu da APC na neman kotun sauraren korefe korefen zabe ta janye damar da ta baiwa Tambuwal

-Ahmed Aliyu na neman kotun korafe-korafen zabe ta hana Tambuwal yin binciken kayayyakin zaben na INEC

-Kotun korafe-korafen zaben ta baiwa Tambuwal damar binciken kayan da akayi zaben gwamanan jihar Sakkwato ranar 9 ga watan Maris, 2019

Dan takarar gwamnan jihar Sakkwato a karkashin jam’iyar APC a zaben gwamnan ranar 9 ga watan Maris, 2019 Alhaji Ahmad Aliyu shine ya shigar da kara akan kotun ta hana Aminu Waziri Tambuwal binciken kayayyakin zaben.

Kotun korafe-korafen zaben a farko ta baiwa Tambuwal damar yin binciken kayayyakin zaben da hukumar zaben mai zaman kanta ta kasa (INEC) tayi amfani dasu wurin zaben a ranakun 9 ga watan Maris da kuma 23 ga watan Maris da ake sake yin zaben bayan na farko bai kammalu ba.

Ahmed Aliyu da APC na neman kotun sauraren korefe korefen zabe ta janye damar da ta baiwa Tambuwal
Ahmed Aliyu Sokoto
Asali: UGC

KU KARANTA:Majalisar zartarwa ta tarayya ta ware N970.2m domin gina barikin hukumar kwastam

A damar da aka baiwa masu wakiltar Tambuwal da jam’iyar PDP akwai yancin binciken hadda kayayyakin sirri na hukar zabe.

Jagogaran lauyoyin dake wakiltar Ahmed Aliyu da jam’iyar APC Jacob Ochidi a zaman da kotun tayi yau Alhamis ya nemi a soke wannan damar da aka baiwa Tambuwal na yin bincken wadannan kayayyaki saboda akwai kayayyakin aiki na sirri a ciki.

Ochidi ya roki kotun ta dage sauraron wannan kara, inda yake cewa basu da halin cigaba da kalubalantar karar saboda karancin lokacin da suka samu kafin zuwa wannan zama.

“ A matsayinmu na masu korafi, muna da niyyar tattara bayanai masu kunshe da hujjoji wanda zamu gabatarwa kotu. Mataki uku wannan abin zai biyo kafin zuwa gaban wannan kotun a ranar da aka bukace shi. A jiya ne kuma muka samu wannan takarda a don haka muna bukatar karin lokaci.” Inji Ochidi.

Da yake karin bayani akan abinda Ochidi yace, Barrister Abdulhamid Zubair cewa yayi “ Muna son a rage daga cikin ababen da aka baiwa Tambuwal damar aiwatarwa saboda sunyi tsauri da yawa kuma sun sabawa kudurin kotun korafe-korafen zabe.” A cewar Abdulhamid.

Ku biyo mu a https://facebook.com/legitnghausa

ko a http://twitter.com/legitcomhausa

KU LATSA: Hanyar sauko da sabuwar manhajar jaridar Legit.com Hausa cikin sauki

Ga masu shawara ko korafi, a same mu a labaranhausa@corp.legit.com

Sanarwa na musamman: Shafin NAIJ Hausa ya koma Legit Hausa

Asali: Legit.ng

Online view pixel