Harin kwalejin Filato: An sako yar uwar mataimakin rajistaran kwalejin da aka sace

Harin kwalejin Filato: An sako yar uwar mataimakin rajistaran kwalejin da aka sace

-Abigail Amos ta kubuta daga hannun masu garkuwa da mutane bayan da aka biya kudin fansa

-Mataimakin rajistaran kwalejin wanda yake yaya a gareta ya tabbar da gaskiyar wannan zance

Kanwar mataimakin rajistaran Kwalejin fasaha da kere-kere ta Filato mai suna Abigail Amos ta kubuta daga hannun wadanda suka saceta a ranar Litinin.

Abigail wacce ke shekarar farko a matakin diploma a kwalejin ta shiga hannun masu garkuwa da mutane ne yayinda suka kawo wani farmaki a sashen gidajen ma’aikatan kwalejin dake unguwar Heipang dake Barikin Ladi da misalin karfe 12:10 na dare.

Harin kwalejin Filato: An sako yar uwar mataimakin rajistaran kwalejin da aka sace
Harin kwalejin Filato: An sako yar uwar mataimakin rajistaran kwalejin da aka sace
Asali: Twitter

KU KARANTA:Ana ci gaba da ragargazar Buhari kan furucin da yayi game da tsaro

Ta kasance tana bacci tare da sauran iyalan gidan mataimakin rajistaran a lokacin da wannan abu ya faro.

Rahotanni sun nuna cewa an sako wannan dalibar ne bayan an biya kudin fansa a daren Litinin kuma aka daukota daidai Kwalejin yan sanda dake Jos inda masu garkuwar suka ajiye ta.

Mataimakin rajistaran, Ezekiel Rangs ya tabbatar da wannan labari a garin Jos ranar Talata.

Rangs yace: “ Hakika mun samu cetota. Ni da kaina na daukota kusa da Kwalejin yan sanda ta Jos da misalin karfe 7:30 na maraice.

“ Mun biya kudin fansa kafin su amince da sakota, amma ba zan so fadin ko nawa bane saboda ina kokarin mantawa ne faruwar wannan lamari.

“ Ta kuma shaida mana cewa ba’a doketa ko kuma cimata zarafi ba yayinda take tsare karkashin masu garkuwar. Mun godema Allah da basu kasheta ba kuma a yanzu ta dawo mana lafiya kalau.”

Ku biyo mu a https://facebook.com/legitnghausa

ko a http://twitter.com/legitcomhausa

KU LATSA: Hanyar sauko da sabuwar manhajar jaridar Legit.com Hausa cikin sauki

Ga masu shawara ko korafi, a same mu a labaranhausa@corp.legit.com

Sanarwa na musamman: Shafin NAIJ Hausa ya koma Legit Hausa

Asali: Legit.ng

Authors:
Mudathir Ishaq avatar

Mudathir Ishaq Mudathir Ishaq is the head of the Hausa desk at Legit.ng. He studied Industrial Chemistry as first degree at the University of Abuja, Journalism (CSR Specialization) with the Michigan State University and runs MSc Industrial Chemistry from the Nasarawa State University, Keffi. With more than a decade experience in news reporting and content editing, he has interviewed influential personalities. He can be reached on: mudathir.ishaq@corp.legit.ng