Wata uwar yara 8 mai shekara 45 ta samu digiri na uku daga jami’ar Usman Dan Fodio

Wata uwar yara 8 mai shekara 45 ta samu digiri na uku daga jami’ar Usman Dan Fodio

- Wata uwar yara 8 mai shekara 45, Halima Usman ta samu digiri na uku daga jami’ar Usman Dan Fodio

- Halima wacce ta kasance yar asalin jihar ta samu wannan digirin ne a fannin lissafi

- Gwamnatin jihar Kebbi ce ta bayyana wannan abun alfaharin a shafinta na Twitter domin taya ta farin ciki

Wata mata yar shekara 45 wacce ta haifi yara takwas daga jihar Kebbi, Halima Usman, ta kammala karamin digiri na uku a fannin lissafi.

An bayyana hakan ne a shafin Twitter na gwamnatin jihar Kebbi, @KBStGovt, a ranar Lahadi, 12 ga watan Afrilu.

Legit.ng tattaro cewa Halima ta mallaki wannan kwali na digiri na uku ne daga jami’ar Usman Dan Fodio sannan an bata takardar ne a lokacin bikin yaye daliban makarantar na 2019.

Kalli hotunan a kasa:

Wata uwar yara 8 mai shekara 45 ta samu digiri na uku daga jami’ar Usman Dan Fodio
Halima Usman cikin shigarta na kammala karatu
Asali: Twitter

Wata uwar yara 8 mai shekara 45 ta samu digiri na uku daga jami’ar Usman Dan Fodio
Halima tare da wasu daga cikin yaranta
Asali: Twitter

Wata uwar yara 8 mai shekara 45 ta samu digiri na uku daga jami’ar Usman Dan Fodio
Halima tare da wani da ake ganin mijinta nee
Asali: Twitter

A halin da ake ciki, a baya Legit.ng ta ruwaito cewa wata mata mai suna Ochuwa Momoh George, mai yara hudu, ta samu digiri na uku daga jami’ar Lagas.

KU KARANTA KUMA: Fashi: Ministan tsaro yace furucinsa baya nufin kaskanta sarakunan gargajiya

Matar wacce ta cika da farin ciki ta je shafin Facebook domin bayyana farin ciki a wannan tafiya tata na mallakar takarar da sakamako mafi daraja.

Idan kuna da wata shawara ko bukatar bamu labari, Tuntube mu a: labaranhausa@corp.legit.ng

Latsa wannan domin samun sabuwar manhajar labarai ta Legit.ng Hausa a wayar ku ta hannu: https://play.google.com/store/apps/details?id=com.naij.hausa&hl=en

Ku biyo mu a shafukanmu na dandalin sada zumunta:

Facebook: https://facebook.com/legitnghausa

Twitter: https://twitter.com/legitnghausa

Muhimmiyar sanarwa: Shafin NAIJ.com Hausa ya koma LEGIT.ng Hausa. Mun gode da kasancewa tare da mu.

Asali: Legit.ng

Authors:
Mudathir Ishaq avatar

Mudathir Ishaq Mudathir Ishaq is the head of the Hausa desk at Legit.ng. He studied Industrial Chemistry as first degree at the University of Abuja, Journalism (CSR Specialization) with the Michigan State University and runs MSc Industrial Chemistry from the Nasarawa State University, Keffi. With more than a decade experience in news reporting and content editing, he has interviewed influential personalities. He can be reached on: mudathir.ishaq@corp.legit.ng