Sabon sarkin Lafia zai shiga fada a gobe Juma'a

Sabon sarkin Lafia zai shiga fada a gobe Juma'a

- Sabon sarkin Lafia, Justis Sidi Dauda Bage, zai shiga fadar Lafia a gobe Juma’a

- Justis Sidi zai baro gidansa da ke Abuja zuwa masarautar na Lafia

- Ana sanya ran alkalin zai shiga fada, sannan kuma ya gudanar da Sallar Juma’a na farko a matsayin sarki a babbar masallacin Juma’a da ke fadar

Sabon sarkin Lafia, Justis Sidi Dauda Bage, zai shiga fadar Lafia a gobe Juma’a, 5 ga watan Afrilu, jaridar Daily Trust ta ruwaito.

Wani hadimin sabon sarkin ya bayyana cewa an kammala shiri tsaf domin komawar sarkin fada daga Abuja, inda yake alkalanci a kotun koli, sannan ya kama mulki a matsayin sarkin Lafia na 17.

Sabon sarkin Lafia zai shiga fada a gobe Juma'a
Sabon sarkin Lafia zai shiga fada a gobe Juma'a
Asali: UGC

Majiyar ta kara da cewa masu rike da sarauta da dama a Lafia sun yi tattaki zuwa Abuja domin kwasar gaisuwa a wajen sabon sarkin.

Ana sanya ran alkalin zai shiga fada a matsayin sarki, sannan ya samu karramawa na musamman daga masu rike da mukamai, hakimai sannan kuma ya gudanar da Sallar Juma’a na farko a matsayin sarki a babbar masallacin Juma’a da ke fadar.

KU KARANTA KUMA: EFCC ta cafke zunzurutun kudi har N54m a filin jirgin sama na Maiduguri

Idan za ku tuna an sanar da Justis Sidi Dauda Bage a matsayin sarkin Lafia na 17 a ranar 26 ga watan Maris, 2019 bayan mutuwar marigayi sarki, Alhaji Isa Mustapha Agwai, a ranar 10 ga watan Janairu, yana da shekaru 84 bayan ya shafe shekaru 44 yana sarauta.

Idan ka na da wata shawara ko bukatar ba mu labari, a tuntube mu a: labaranhausa@corp.legit.ng

Ku same mu a https://www.facebook.com/legitnghausa

Ko a http://twitter.com/legitnghausa

Latsa wannan domin samun sabuwar manhajar labarai ta LEGIT NG Hausa a wayar ku ta hannu: https://play.google.com/store/apps/details?id=com.naij.hausa

Shafin NAIJ Hausa ya koma LEGIT

Asali: Legit.ng

Authors:
Mudathir Ishaq avatar

Mudathir Ishaq Mudathir Ishaq is the head of the Hausa desk at Legit.ng. He studied Industrial Chemistry as first degree at the University of Abuja, Journalism (CSR Specialization) with the Michigan State University and runs MSc Industrial Chemistry from the Nasarawa State University, Keffi. With more than a decade experience in news reporting and content editing, he has interviewed influential personalities. He can be reached on: mudathir.ishaq@corp.legit.ng