Majalisar dinkin duniya ta fara yakar masu kyamar Musulmi a duniya

Majalisar dinkin duniya ta fara yakar masu kyamar Musulmi a duniya

Majalisar dinkin duniya ta yi jan kunne akan yadda matsalar kyamar Musulmi kara zafafa a duniya. Wannan jan kunne na zuwa ne a kasa da wata guda bayan kaiwa Muslulmi mumunan hari a kasar New Zealand wanda yayi sanadiyar mutuwar mutum 50 a masallatai biyu.

Babban sakataren majalisar, Antonio Guterres ne ya bayyana hakan a wani jawabi da ya gabatar a jami’ar Al-Azhar da kekasar Masar, yayinda yake zantawa da Shugaban jami’ar, Sheik Ahmed al-Tayeb.

Guterres ya ce, duniya na fama da matsalar tsananin kyamar Musulmi da kyamar Yahudawa da nuna wariyar launin fata har ma da kyamar baki.

Majalisar dinkin duniya ta fara yakar masu kyamar Musulmi a duniya
Majalisar dinkin duniya ta fara yakar masu kyamar Musulmi a duniya
Asali: UGC

Sakataren ya tabo batun harin da wani mai rajin fifita farar fata ya kai a Masallatan New Zealand da kuma harin da aka kai wa Yahudawa a Majami’arsu da ke Pittsburgh, harin da aka bayyana a matsayin mafi muni kan Yahudawa a tarihin Amurka.

KU KARANTA KUMA: Yanzu Yanzu: Kungiyar ASUU reshen jiha ta sanar da shiga yajin aikin sai baba-ya-gani

Guterres da ke ziyarar kwanaki biyu a Masar, zai gana da shugaban kasar Abdel Fattah al-Sisi.

A wani lamari na daban, Legit.ng ta rahaoto cewa Shugaban hukumar lafiya na jihar Niger, Usman Ndanusa, ya tabbatar da mutuwar mutane takwas, wanda cutar Sankarau ta kashe a karamar hukumar Borgu da ke jihar Niger.

Mista Ndanusa, wanda ya ke likita, shine ya bayyana hakan a lokacin da ya ke tattaunawa da kamfanin dillancin labarai na Najeriya a yau Laraba 3 ga watan Afrilu, a garin Minna babban birnin jihar.

Muhimmiyar sanarwa: Shafin NAIJ.com Hausa ya koma LEGIT.ng Hausa. Mun gode da kasancewarku tare da mu.

Latsa wannan domin samun sabuwar manhajar labarai ta Legit.ng Hausa a wayar ku ta hannu: : https://play.google.com/store/apps/details?id=com.naij.hausa&hl=en

Ku biyo mu a shafukanmu na dandalin sada zumunta:

Facebook: https://facebook.com/legitnghausa

Twitter: https://twitter.com/legitnghausa

Idan kuna da wata shawara ko bukatar bamu labari, Tuntube mu a: labaranhausa@corp.legit.ng

Asali: Legit.ng

Authors:
Mudathir Ishaq avatar

Mudathir Ishaq Mudathir Ishaq is the head of the Hausa desk at Legit.ng. He studied Industrial Chemistry as first degree at the University of Abuja, Journalism (CSR Specialization) with the Michigan State University and runs MSc Industrial Chemistry from the Nasarawa State University, Keffi. With more than a decade experience in news reporting and content editing, he has interviewed influential personalities. He can be reached on: mudathir.ishaq@corp.legit.ng