Da duminsa: Buhari ya isa kasar Senegal (Hotuna)

Da duminsa: Buhari ya isa kasar Senegal (Hotuna)

Shugaba Muhammadu Buhari ya dira Dakar, babar birnin kasar Senegal da daren Litinin, 2 ga watan Afrilu, 2019 inda aka gayyacesa a matsayin babban bako na musamman a bikin rantsar da shugaban kasar Senegal, Macky Sall.

Mun kawo muku rahoton cewa tafiyarsa na farko bayan nasara a zaben shugaban kasa, Shugaba Muhammadu Buhari zai garzaya kasar Senegal domin amsa goron gayyatar shugaban kasar, Macky Sall, wanda za'a rantsar a zangoo na biyu ranan Talata, 2 ga watan Afrilu,2019.

Da duminsa: Buhari ya isa kasar Senegal (Hotuna)
Buhari ya isa
Asali: Facebook

Legit.ng ta samu wannan rahoton daga fadar shugaban kasa da safiyar Litinin, 1 ga watan Afrilu inda ta ce:

"Shugaba Muhammadu Buhari zai bar Abuja yau domin zuwa Dakar, birnin Senegal domin halartan bikin rantsar da shugaban kasar Senegal Macky Sall, bayan nasarar da ya samu a zaben shugaban kasa karo na biu.

"Domin amsa goron gayyatar shugaban kasan, shugaba Buhari wanda shine shugaba kungiyar ECOWAS zai zama babban bako tare da sauran shugabannin nahiyar Afrika a cibiyar Diamniadio ranar Talata."

Shugaban kasa zai tafi tare sa gwamnan jihar Bauchi, Mohammed Abubakar; gwamnan jihar Kaduna, Nasir El-Rufa'i; da gwamnan jihar Nasarawa, Umaru Tanko AlMakura."

Sauran sune ministan harkokin wajen Najeriya, Geoffrey Onyeama; mai shawarar tsaron kasa, Babagana Munguno; shugaban hukumar NIA, Amb ahmed Rufa'i da sauransu.

Da duminsa: Buhari ya isa kasar Senegal (Hotuna)
Da duminsa: Buhari ya isa kasar Senegal (Hotuna)
Asali: Facebook

Da duminsa: Buhari ya isa kasar Senegal (Hotuna)
Da duminsa: Buhari ya isa kasar Senegal (Hotuna)
Asali: Facebook

Muhimmiyar sanarwa: Shafin NAIJ.com Hausa ya koma LEGIT.ng Hausa. Mun gode da kasancewarku tare da mu.

Latsa wannan domin samun sabuwar manhajar labarai ta Legit.ng Hausa a wayar ku ta hannu:

https://play.google.com/store/apps/details?id=com.naij.hausa

Ku biyo mu a shafukanmu na dandalin sada zumunta:

Facebook: https://facebook.com/legitnghausa

Twitter: https://twitter.com/legitnghausa

Idan kuna da wata shawara ko bukatar bamu labari,

Tuntube mu a: labaranhausa@corp.legit.ng

Asali: Legit.ng

Online view pixel