Da duminsa: Buhari ya isa kasar Senegal (Hotuna)

Da duminsa: Buhari ya isa kasar Senegal (Hotuna)

Shugaba Muhammadu Buhari ya dira Dakar, babar birnin kasar Senegal da daren Litinin, 2 ga watan Afrilu, 2019 inda aka gayyacesa a matsayin babban bako na musamman a bikin rantsar da shugaban kasar Senegal, Macky Sall.

Mun kawo muku rahoton cewa tafiyarsa na farko bayan nasara a zaben shugaban kasa, Shugaba Muhammadu Buhari zai garzaya kasar Senegal domin amsa goron gayyatar shugaban kasar, Macky Sall, wanda za'a rantsar a zangoo na biyu ranan Talata, 2 ga watan Afrilu,2019.

Da duminsa: Buhari ya isa kasar Senegal (Hotuna)
Buhari ya isa
Asali: Facebook

Legit.ng ta samu wannan rahoton daga fadar shugaban kasa da safiyar Litinin, 1 ga watan Afrilu inda ta ce:

"Shugaba Muhammadu Buhari zai bar Abuja yau domin zuwa Dakar, birnin Senegal domin halartan bikin rantsar da shugaban kasar Senegal Macky Sall, bayan nasarar da ya samu a zaben shugaban kasa karo na biu.

"Domin amsa goron gayyatar shugaban kasan, shugaba Buhari wanda shine shugaba kungiyar ECOWAS zai zama babban bako tare da sauran shugabannin nahiyar Afrika a cibiyar Diamniadio ranar Talata."

Shugaban kasa zai tafi tare sa gwamnan jihar Bauchi, Mohammed Abubakar; gwamnan jihar Kaduna, Nasir El-Rufa'i; da gwamnan jihar Nasarawa, Umaru Tanko AlMakura."

Sauran sune ministan harkokin wajen Najeriya, Geoffrey Onyeama; mai shawarar tsaron kasa, Babagana Munguno; shugaban hukumar NIA, Amb ahmed Rufa'i da sauransu.

Da duminsa: Buhari ya isa kasar Senegal (Hotuna)
Da duminsa: Buhari ya isa kasar Senegal (Hotuna)
Asali: Facebook

Da duminsa: Buhari ya isa kasar Senegal (Hotuna)
Da duminsa: Buhari ya isa kasar Senegal (Hotuna)
Asali: Facebook

Muhimmiyar sanarwa: Shafin NAIJ.com Hausa ya koma LEGIT.ng Hausa. Mun gode da kasancewarku tare da mu.

Latsa wannan domin samun sabuwar manhajar labarai ta Legit.ng Hausa a wayar ku ta hannu:

https://play.google.com/store/apps/details?id=com.naij.hausa

Ku biyo mu a shafukanmu na dandalin sada zumunta:

Facebook: https://facebook.com/legitnghausa

Twitter: https://twitter.com/legitnghausa

Idan kuna da wata shawara ko bukatar bamu labari,

Tuntube mu a: labaranhausa@corp.legit.ng

Asali: Legit.ng

Authors:
Mudathir Ishaq avatar

Mudathir Ishaq Mudathir Ishaq is the head of the Hausa desk at Legit.ng. He studied Industrial Chemistry as first degree at the University of Abuja, Journalism (CSR Specialization) with the Michigan State University and runs MSc Industrial Chemistry from the Nasarawa State University, Keffi. With more than a decade experience in news reporting and content editing, he has interviewed influential personalities. He can be reached on: mudathir.ishaq@corp.legit.ng