Zaben Sokoto: APC ta samu kujeru 16 yayin da PDP ta samu 14 a majalisar dokoki

Zaben Sokoto: APC ta samu kujeru 16 yayin da PDP ta samu 14 a majalisar dokoki

Sakamakon zaben 2019 zuwa ga kujeru 30 na majalisar dokokin jihar Sokoto ya bayyana cewa a majalisar dokokin jihar ta 9, jam'iyyar APC ta samu kujeru 16 yayin da jam'iyyar PDP ta samu kujeru 14.

Ga mambobin majalisar ta 8 a jihar Sokoto, akwai mambobi 19 na PDP, wadanda 10 daga cikinsu suka fadi zaben 2019, yayin da guda daya bai ma tsaya takara ba.

Mamban da bai tsaya takarar kujerar majalisar dokokin jihar ba shi ne kakakin majalisar, Salihu Maidaji wanda ke wakiltar mazabar Gada ta Gabas.

KARANTA WANNAN: Rahoto na musamman: Adadin kudaden da PENCOM ta tara ya kai Naira tiriliyan 8.67

A mai makon hakan, ya tsaya takarar kujerar sanatan mazabar Sokoto ta Gabas amma ya sha kasa a hannun sanatan mazabar mai ci Ibrahim Gobir na jam'iyyar APC.

Ga sunayen 'yan majalisun dokokin da mazabunsu tare da jam'iyyunsu:

1) Aminu Magaji APC- Dange/Shuni

2) Mustapha Abdullahi APC- Sokoto South 1

3)Malami Ahmed PDP- Sokoto South II

4) Suke Romo PDP- Tambuwal West

5) Mode Ladan PDP Tambuwal East

6)Musa Miko PDP- Tangaza

7) Murtala Maigona APC- Wamakko

8) Aminu Achida APC-Wurno

9) Shehu Yabo APC- Yabo

10) Haliru Buhari PDP- Sokoto North 1

11) Ibrahim Arzika PDP- Sokoto North II

12) Abdullahi Randa PDP- Tureta

13) Umaru Sahabi PDP- Binji

14) Abubakar Magaji PDP- Bodinga North

15) Bala Tukur APC- Bodinga South

16) Altine Kyadawa APC- Gada West

17) Kabiru Dauda APC- Bada East

18) Mustapha Balle PDP- Gudu

19) Bello Idris APC- Gwadabawa South

20) Abdullahi Garba APC- Gwadabawa North

21) Bello Ambarura APC- Illela

22) Habibu Modachi PDP- Isa

23) Abdullahi Mahmud PDP- Kware

24) Abdullahi Zakari APC- Rabah

25) Almustapha Aminu PDP- Sabon Birni North

26) Saidu Ibrahim APC- Sabon Birni South

27) Alhaji Maidawa APC- Shagari

28) Atiku Liman PDP- Silame

29) Isa Harisu APC- Kebbe

30) Faruku Amadu APC- Goronyo

SANARWA: Shafin jaridar NAIJ.com Hausa ya sauya suna zuwa Legit.ng Hausa. Muna fatan za ka ci gaba da kasancewa tare da Legit.ng Hausa don karanta labarai da dumi duminsu.

Latsa wannan domin samun sabuwar manhajar labarai ta Legit.ng Hausa a wayarku ta hannu: https://play.google.com/store/apps/details?id=com.naij.hausa

Ku biyo mu a shafukan mu na dandalin sada zumunta:

Facebook: https://facebook.com/legitnghausa

Twitter: https://twitter.com/legitnghausa

Idan kuna da wata shawara ko bukatar bamu labari, Tuntube mu a: labaranhausa@corp.legit.ng

Asali: Legit.ng

Online view pixel