Siyasar Zamfara: Maganar rikicin jam'iyyar APC a Zamfara ta sake tasowa

Siyasar Zamfara: Maganar rikicin jam'iyyar APC a Zamfara ta sake tasowa

Kotun daukaka kara mai zaman ta a jihar Sokoto da ta sake dage sauraren shari'ar dake gaban ta na rikicin jam'iyyar APC a jihar Zamfara bayan da bangaren da ya shigar da karar ya ce bai yadda da alkalan kotun ba sam-sam.

Kamar dai yadda muka samu, bangaren Sanata Marafa ne ya daukaka kara a Sokoto domin kalubalantar hukuncin da kotun tarayya a Gusau ta zartar cewa an yi zaben fitar da 'yan takara na jam'iyyar APC a Zamfara.

Siyasar Zamfara: Maganar rikicin jam'iyyar APC a Zamfara ta sake tasowa
Siyasar Zamfara: Maganar rikicin jam'iyyar APC a Zamfara ta sake tasowa
Asali: UGC

KU KARANTA: Sarkin Kano ya jinjinawa Kwamishinan 'yan sanda Wakili

Karar da aka dage dai na zuwa ne bayan kammala zaben gwamna a Zamfara inda hukumar zabe ta sanar da Muktar Shehu Idris dan takarar bangaren gwamnati a jam'iyyar APC da ake kalubalanta a matsayin wanda ya lashe zaben.

A baya dai kamar yadda muka samu, wata kotun daukaka kara ce dake a Abuja ta bai wa INEC umurnin ta amince da 'yan takarar APC a Zamfara, bayan da a farko INEC ta ki amincewa da 'yan takarar jam'iyyar saboda ta gaza yin zaben fitar da 'yan takara.

Rikicin na APC a Zamfara ya samo asali ne bayan da Gwamna Abdulaziz Yari ya sanar da goyon bayansa ga kwamishinansa na kudi, Alhaji Muktar Shehu Idris, a matsayin wanda zai gaje shi.

Muhimmiyar sanarwa: Shafin NAIJ.com Hausa ya koma legit.ng Hausa. Mun gode da kasancewarku tare da mu.

Latsa wannan domin samun labarai a wayar ku ta hannu: https://play.google.com/store/apps/details?id=com.naij.hausa

Ku biyo mu a shafukanmu na dandalin sada zumunta:

Facebook: https://web.facebook.com/legitnghausa?_rdc=1&_rdr

Twitter: https://twitter.com/legitnghausa

Idan kuna da wata shawara ko bukatar bamu labari,

Tuntube mu a: labaranhausa@corp.legit.com

Asali: Legit.ng

Authors:
Mudathir Ishaq avatar

Mudathir Ishaq Mudathir Ishaq is the head of the Hausa desk at Legit.ng. He studied Industrial Chemistry as first degree at the University of Abuja, Journalism (CSR Specialization) with the Michigan State University and runs MSc Industrial Chemistry from the Nasarawa State University, Keffi. With more than a decade experience in news reporting and content editing, he has interviewed influential personalities. He can be reached on: mudathir.ishaq@corp.legit.ng