Zaben 2019: Jam'iyyar APC ta lashe rumfar Shugaba Buhari da gagarumin rinjaye

Zaben 2019: Jam'iyyar APC ta lashe rumfar Shugaba Buhari da gagarumin rinjaye

Jam'iyya mai mulki ta All Progressives Congress (APC) a jihar Katsina ta lashe zaben gwamna da na dan majalisar jiha a rumfar shugaban kasa, Muhammadu Buhari.

Sakamakon zaben rumfar da muka samu na rumfar shugaban kasar watau rumfar ta 003, a mazabar Sarkin Yara A ta jihar Daura na nuni ne da cewa jam'iyyar ta APC ta lashe zaben ne da gagarumin rinjaye.

Zaben 2019: Jam'iyyar APC ta lashe rumfar Shugaba Buhari da gagarumin rinjaye
Zaben 2019: Jam'iyyar APC ta lashe rumfar Shugaba Buhari da gagarumin rinjaye
Asali: Facebook

KU KARANTA: Sakamakon zaben gwamna da 'yan majalisa a Zamfara da Katsina

Legit.ng Hausa ta samu cewa Gwamnan jihar ta Katsina, Aminu Bello Masari na jam'iyyar APC samu kuri'u 370 yayin da dan takarar gwamna a jam'iyyar PDP, Sanata Yakubu Lado Danmarke ya samu kuri'u 42 kacal.

Haka ma dai a zaben kujerar dan majalisar jiha jam'iyyar APC ta samu kuri'u 368 yayin da ita kuma PDP ta samu kuri'u 42.

A wani labarin kuma, Akalla mutane takwas ne suka jikkata a yayin wani artabu a tsakanin magoya bayan manyan jam'iyyun Peoples Democratic Party (PDP) da kuma All Progressives Congress (APC) a mazaba ta 9 rumfa ta 007 a karamar hukumar nsit Atai, jihar Akwa Ibom.

Sai dai bayanan kuma rahotannin da muke samu daga majiyoyin mu sun bayyana mana cewa mafiya yawan wadanda suka ji raunin a sakamakon fadan 'yan jam'iyyar APC kuma tuni har an kai su wata asibi mafi kusa domin karbar kulawar likita.

Muhimmiyar sanarwa: Shafin NAIJ.com Hausa ya koma legit.ng Hausa. Mun gode da kasancewarku tare da mu.

Latsa wannan domin samun labarai a wayar ku ta hannu: https://play.google.com/store/apps/details?id=com.naij.hausa

Ku biyo mu a shafukanmu na dandalin sada zumunta:

Facebook: https://web.facebook.com/legitnghausa?_rdc=1&_rdr

Twitter: https://twitter.com/legitnghausa

Idan kuna da wata shawara ko bukatar bamu labari,

Tuntube mu a: labaranhausa@corp.legit.com

Asali: Legit.ng

Authors:
Mudathir Ishaq avatar

Mudathir Ishaq Mudathir Ishaq is the head of the Hausa desk at Legit.ng. He studied Industrial Chemistry as first degree at the University of Abuja, Journalism (CSR Specialization) with the Michigan State University and runs MSc Industrial Chemistry from the Nasarawa State University, Keffi. With more than a decade experience in news reporting and content editing, he has interviewed influential personalities. He can be reached on: mudathir.ishaq@corp.legit.ng