Dan Abacha ya ba Buhari tabbacin samun kuri’u miliyan 2

Dan Abacha ya ba Buhari tabbacin samun kuri’u miliyan 2

- Dan takarar gwamna a karkashin inuwar jam’iyyar Advance Peoples Democratic Alliance (APDA) a jihar Kano, Mohammed Abacha ya nuna goyon bayansa ga kudirin tazarcen Shugaba Buhari

- Mohammed yayi alkawarin kawo wa Shugaban kasar akalla kuri’u miliyan biyu a jihar

- Yace yana goyon bayan Buhari saboda tarin nasarorin da ya samu tun bayan hawarsa karagar mulki

Mohammed Abacha, dan takarar gwamna a karkashin inuwar jam’iyyar Advance Peoples Democratic Alliance (APDA) a jihar Kano ya nuna goyon bayansa ga kudirin tazarcen Shugaban kasa Muhammadu Buhari.

Mohammed yayi alkawarin kawo wa Shugaban kasar akalla kuri’u miliyan biyu a jihar.

Dan Abacha ya ba Buhari tabbacin samun kuri’u miliyan 2
Dan Abacha ya ba Buhari tabbacin samun kuri’u miliyan 2
Asali: Getty Images

Baban dan marigayi tsohon shugaan kasar, Janar Sani Abacha ya kaddamar da goyon bayan dan takarar Shugaban kasar na jam’iyyar All Progressives Congress (APC) a bainar jama’a, yayinda yake jawabi ga manema labarai a ofishin kamfen dinsa da ke hanyar Maguwa a Kano a ranar Litinin, 18 ga watan Fabrairu.

KU KARANTA KUMA: Atiku zai kayar da Buhari da tazara mafi girma – Kungiyar kamfen tayi ikirari

Da farko dai dama jam’iyyar APDA na kasa ta kaddanar da goyon bayanta ga tazarcen Shugaban kasa.

Abacha, wanda ya samu wakilcin Bashir Bataya, Shugaban APDA a Kano, ya nuna goyon bayansa ga Buhari saboda tarin nasarorin da ya samu tun bayan hawarsa karagar mulki.

A cewarsa wasu daga cikin nasarorin Buhari sun hada da tsaro, daidaita tattalin arziki, manyan ayyuka da kuma habbaka harkar noma.

Sanarwa: Ku ci gaba da kasancewa tare da mu yayin da Shafin Naij.com Hausa ya sauya suna zuwa Legit.ng Hausa

Latsa wannan domin samun sabuwar manhajar labarai ta Legit.ng Hausa a wayarku ta hannu: https://play.google.com/store/apps/details?id=com.naij.hausa

Domin shawara ko bukatar bamu labari, tuntube mu a: labaranhausa@corp.legit.com

Ku biyo cikin shafukan mu na zaurukan sada zumunta:

https://facebook.com/legitnghausa

https://twitter.com/legitnghausa

Asali: Legit.ng

Authors:
Mudathir Ishaq avatar

Mudathir Ishaq Mudathir Ishaq is the head of the Hausa desk at Legit.ng. He studied Industrial Chemistry as first degree at the University of Abuja, Journalism (CSR Specialization) with the Michigan State University and runs MSc Industrial Chemistry from the Nasarawa State University, Keffi. With more than a decade experience in news reporting and content editing, he has interviewed influential personalities. He can be reached on: mudathir.ishaq@corp.legit.ng