Kwankwaso ya yi godiya ga mutanen Kano kan yadda suka yi tururuwar fitowa kamfen din PDP
- Sanata Rabi’u Kwankwaso ya yaba ma mutanen Kano kan tururuwar fitowa da suka yi a gangamin kamfen din dan takarar shugaban kasa na PDP da ya gudana a filin wasa na Sani Abacha a ranar 10 ga watan Fabrairu
- Kwankwaso ya mika godiyan ne yayinda yake jawabi ga malaman addinin Musulunci da suka kai masa ziyarar ban girma gidansa da ke Kano
- Tsohon gwamnan na jihar Kano, ya bayyana cewa dandazon da suka hallara a wajen gangamin ya nuna karara cewa mutanen Kano na PDP ne
Sanata mai wakiltan yankin Kano ta tsakiya a majalisar dokokin kasar, Alhaji Rabi’u Kwankwaso ya yaba ma mutanen Kano kan tururuwar fitowa da suka yi a gangamin kamfen din dan takarar shugaban kasa na PDP da ya gudana a filin wasa na Sani Abacha a ranar 10 ga watan Fabrairu.
Kwankwaso ya mika godiyan ne yayinda yake jawabi ga malaman addinin Musulunci da suka kai masa ziyarar ban girma gidansa da ke Kano a daren ranar Alhamis, 14 ga watan Fabrairu.
Kwankwaso wanda ya kasance tsohon gwamnan jihar Kano, ya bayyana cewa dandazon da suka hallara a wajen gangamin ya nuna karara cewa mutanen Kano na PDP.
Ya shawarci malaman Musulunci a jihar da su guji tsoma baki cikin siyasa maimakon haka suyi amfani da matsayinsu na malaman addini su shawarci mutanensu kan yadda za su samu shugabanci nagari.
KU KARANTA KUMA: Saraki yayi kuskuren nema wa shugaba Buhari kuri’u 90% a Kwara (bidiyo)
Ya yi kira ga mutanen Kano da su zabi yan takarar PDP a dukkan matakai, inda ya kara fa cewa masu zabe suyi amfani da zuciyarsu wajen zabar yan takara da shugabanni nagari, tare da hangen nesa.
Muhimmiyar sanarwa: Shafin NAIJ.com Hausa ya koma LEGIT.ng Hausa. Mun gode da kasancewarku tare da mu.
Latsa wannan domin samun sabuwar manhajar labarai ta Legit.ng Hausa a wayar ku ta hannu: https://play.google.com/store/apps/details?id=com.naij.hausa
Ku biyo mu a shafukanmu na dandalin sada zumunta:
Facebook: https://facebook.com/legitnghausa
Twitter: https://twitter.com/legitnghausa
Idan kuna da wata shawara ko bukatar bamu labari, Tuntube mu a: labaranhausa@corp.legit.ng
Asali: Legit.ng