Baki-ke-yanka-wuya: Wani jigon PDP a Kaduna ya furta kalaman da suka jefa shi a tsomomuwa

Baki-ke-yanka-wuya: Wani jigon PDP a Kaduna ya furta kalaman da suka jefa shi a tsomomuwa

Wani jigo a jam’iyyar PDP na jihar Kaduna da shine darektan yada labaran jam’iyyar, ya yi kira ga magoya bayan jam’iyyar a jihar Kaduna da su lakadawa duk wanda ya zabi wata jam’iyya da ba jam’iyyar PDP ba dukan tsiya sannan su tabbata sun kwana da shirin ko ta kwana a jihar.

Ben Bako ya bayyana haka ne a taron kamfen din jam’iyyar a garin Kafanchan.

Baki-ke-yanka-wuya: Wani jigon PDP a Kaduna ya furta kalaman da suka jefa shi a tsomomuwa
Baki-ke-yanka-wuya: Wani jigon PDP a Kaduna ya furta kalaman da suka jefa shi a tsomomuwa
Asali: UGC

KU KARANTA: Wani dan Arewa ya kera jirgin sama

Legit.ng Hausa da ta ga bidiyon Bako ya kara da cewa duk wanda ya tare su a hanya a lokacin da suke dakon kuri’u daga kauyukan su su tabbata sun yi masa dukan tsiya sannan su yi ta haka har sai sun iso garin Kafanchan inda za a tattara kuri’u.

Idan ba a manta ba a irin haka ne gwamnan jihar Kaduna Nasir El-Rufai shima ya zaro wasu kalamai inda yake cewa duk wanda ya saka wa Najeriya baki a harkokin zaben ta za a koma gida da gawar sa. Wannan magana ya tada wa mutane da dama hankali da har sai da gwamna El-Rufai ya fito ya wanke kansa, Cewa ba abinda yake nufi ba kenan.

Sai dai kuma shugaban Kasa Muhammadu Buhari ya bayyana cewa lallai zai tabbata ba a tada yamutsi a lokacin zabe ba, yana mai cewa burin sa shine ayi zabe lafiya.

Muhimmiyar sanarwa: Shafin NAIJ.com Hausa ya koma legit.ng Hausa. Mun gode da kasancewarku tare da mu.

Latsa wannan domin samun labarai a wayar ku ta hannu: https://play.google.com/store/apps/details?id=com.naij.hausa

Ku biyo mu a shafukanmu na dandalin sada zumunta:

Facebook: https://web.facebook.com/legitnghausa?_rdc=1&_rdr

Twitter: https://twitter.com/legitnghausa

Idan kuna da wata shawara ko bukatar bamu labari,

Tuntube mu a: labaranhausa@corp.legit.com

Asali: Legit.ng

Authors:
Mudathir Ishaq avatar

Mudathir Ishaq Mudathir Ishaq is the head of the Hausa desk at Legit.ng. He studied Industrial Chemistry as first degree at the University of Abuja, Journalism (CSR Specialization) with the Michigan State University and runs MSc Industrial Chemistry from the Nasarawa State University, Keffi. With more than a decade experience in news reporting and content editing, he has interviewed influential personalities. He can be reached on: mudathir.ishaq@corp.legit.ng