Hako man fetur: Jihar Bauchi na gab da zama tamkar jihohin Niger Delta
- Jihar Bauchi da ke yankin arewacin Najeriya na gab da zama tamkar jihohin Niger Delta masu arzikin man fetur
- Ana ci gaba da aikin hako rijiyoyin mai a kauyen Kolmari da ke karamar hukumar Alkaler na jihar Bachi
Rahotanni da ke zuwa mana sun nuna cewa jihar Bauchi da ke yankin arewacin Najeriya na gab da zama tamkar jihohin Niger Delta masu arzikin man fetur.
An tattaro cewa gwamnatin tarayya karkashin jagrancin Shugaban kasa Muhammadu Buhari na ci gaba da aikin hako rijiyoyin mai a kauyen Kolmari da ke karamar hukumar Alkaler na jihar Bachi.
Ga hotunan yadda aikin hako man ke gudana a jihar:
KU KARANTA KUMA: Yanzu Yanzu: Zanga-zanga ya barke a sakatariyar NBA kan dakatar da Onnoghen
A wani lamari na daban, mun ji cewa rundunar sojin Najeriya a karkashin jagorancin Safsan ta, Laftanal Janar Tukur Yusuf Buratai sun soma kera motocin sulke da na yaki manya da kanana domin fuskantar abokan gaba da sauran masu tada kayar baya a kamfanin su dake a jihar Kaduna.
Da yake bude kamfanin, Laftanal Janar Tukur Yusuf Buratai a ranar Asabar din da ta gabata ya ce nan da shekara ta 2030, kamfanin zai soma kerawa sauran kasashen Afrika da ma duniya baki daya motocin.
Muhimmiyar sanarwa: Shafin NAIJ.com Hausa ya koma legit.ng Hausa. Mun gode da kasancewarku tare da mu.
Latsa wannan domin samun labarai a wayar ku ta hannu: https://play.google.com/store/apps/details?id=com.naij.hausa
Ku biyo mu a shafukanmu na dandalin sada zumunta:
Facebook: https://web.facebook.com/legitnghausa?_rdc=1&_rdr
Twitter: https://twitter.com/legitnghausa
Idan kuna da wata shawara ko bukatar bamu labari, tuntube mu a: labaranhausa@corp.legit.ng
Asali: Legit.ng