Jam'iyyar PDP ta samu gagarumin karuwa a jihar Gombe

Jam'iyyar PDP ta samu gagarumin karuwa a jihar Gombe

Jam'iyyar Peoples Democratic Party a jihar Gombe ta samu gagarumin karuwa yayinda akalla mambobin jam'iyyar All Progressives Congress, APC, 3000 suka fita daga jam'iyyar a karamar hukumar Deba dake jihar.

Mambobin jam'iyyar APC daga garuruwan Lubo, Kinafa da Difa sunyi hannun riga da jam'iyyar ne yayinda ake shirye-shiryen zaben shugaban kasa, yan majalisun tarayya da na gwamna a jihar a watan Febrairu, 2019.

Kakakin majalisar dokokin jihar da wasu manyan jami'an gwamnatin jihar sun tarbi wadanda suka sauya sheka. Sun bayyana cewa suna canza jam'iyya ne saboda irin ayyukan zo a gani da gwamnan johar Ibrahim Dankwambo keyi.

KU KARANTA: Atiku makiyin kabilar Fulani ne, kada wanda ya zabeshi - Miyetti Allah Kautal Horey ta yi kira ga mambobinta

A bangare guda, Mambobin jam’iyyar Peoples Democratic Party (PDP) da suka sauya sheka zuwa All Progressives Congress (APC) a kauyen Tika da ke yankin Kuje, sun shugabansu, Abdullahi D. Galadima, cewa sun yi danasanin kuskuren da suka yi a zabar jam’iyyar adawa a zaben da ya gabata.

Wani tsohon shugaban PDP a Tika, Mista Ayi Gyiayegbe, ya bayyana hakan a lokacin da ya jagoranci mambobin PDP 1,245 zuwa APC a jiya, a yankin cewa ba za su maimaita irin wannan kuskuren ba a zaben Fabrairu da Maris.

Yace hukuncin da ya yanke na komawa APC daaga PDP saboda tarin kokarin da gwamnatin Galadima tayi ne a Kuje, inda ya bayyana cewa shugaban ya taimaki mutane da dama a yankin duk da banbancin siyasa.

Muhimmiyar sanarwa: Shafin NAIJ.com Hausa ya koma LEGIT.ng Hausa. Mun gode da kasancewarku tare da mu.

Latsa wannan domin samun sabuwar manhajar labarai ta Legit.ng Hausa a wayar ku ta hannu: https://play.google.com/store/apps/details?id=ng.legit.hausa&hl=en

Ku biyo mu a shafukanmu na dandalin sada zumunta:

Facebook: https://facebook.com/legitnghausa

Twitter: https://twitter.com/legitnghausa

Idan kuna da wata shawara ko bukatar bamu labari,

Tuntube mu a: labaranhausa@corp.legit.ng

Asali: Legit.ng

Authors:
Mudathir Ishaq avatar

Mudathir Ishaq Mudathir Ishaq is the head of the Hausa desk at Legit.ng. He studied Industrial Chemistry as first degree at the University of Abuja, Journalism (CSR Specialization) with the Michigan State University and runs MSc Industrial Chemistry from the Nasarawa State University, Keffi. With more than a decade experience in news reporting and content editing, he has interviewed influential personalities. He can be reached on: mudathir.ishaq@corp.legit.ng