Zaben 2019: Gwamna Masari zai kaddamar da kamfen dinsa a gobe
- Gwamna Aminu Bello Masari zai kaddamar da kamfen dinsa na sake neman kujerar gwamna a karo na biyu
- Za’a gudanar da gagamin siyasar ne a karamar hukumar Funtua da ke jihar Katsina
- Babban sakataren gwamnatin jihar yace babu makawa Masar zai kai labara saboda ayyukan da gwamnatinsa ta yi a fadin jihar
Gwamna Aminu Bello Masari zai kaddamar da kamfen dinsa na sake neman kujerar gwamna a karo na biyu a karamar hukumar Funtua da ke jihar Katsina.
Shugaban kungiyar kamfen din Masari kuma sakataren gwamnatin jihar, Dr Mustapha Inuwa wadanda ya yi jawabi ga taron manema labarai a jiya Alhamis, 27 ga watan Disamba ya ce tawagar kamfen din za su zagaye dukkanin kananan hukumomi 34 da ke jihar.
Ya ce a matsayin su na mambobi masu biyayya ga APC, za su bi dukkanin sharuda da ka’idojin kamfen, inda ya kara da cewa nasarorin da gwamnatin Masari ta samu a kowani bangare na jihar ya isa ya bayar da tabbacin cewa zai yi nasarar yin tazarce.
A cewarsa, za’a kaddamar da dukkaninayyukan da aka kammala a dukka wuraren da za su ziyarta.
KU KARANTA KUMA: Shehu Sani yi martani bayan ikirarin cewa iyalan Buhari na da hannun jari a kamfanoni 2
Ya kuma kara da cewar za kuma su karbi sabbin mambobin siyasa da suka sauya sheka daga sauran jam’iyyun siyasa.
Idan ka na da wata shawara ko bukatar ba mu labari, a tuntube mu a: labaranhausa@corp.legit.ng
Ku same mu a https://www.facebook.com/legitnghausa
Ko a http://twitter.com/legitnghausa
Latsa wannan domin samun sabuwar manhajar labarai ta LEGIT NG Hausa a wayar ku ta hannu: https://play.google.com/store/apps/details?id=com.naij.hausa&hl=en
Shafin NAIJ Hausa ya koma LEGIT
Asali: Legit.ng