Zaben 2019: Gwamna Masari zai kaddamar da kamfen dinsa a gobe

Zaben 2019: Gwamna Masari zai kaddamar da kamfen dinsa a gobe

- Gwamna Aminu Bello Masari zai kaddamar da kamfen dinsa na sake neman kujerar gwamna a karo na biyu

- Za’a gudanar da gagamin siyasar ne a karamar hukumar Funtua da ke jihar Katsina

- Babban sakataren gwamnatin jihar yace babu makawa Masar zai kai labara saboda ayyukan da gwamnatinsa ta yi a fadin jihar

Gwamna Aminu Bello Masari zai kaddamar da kamfen dinsa na sake neman kujerar gwamna a karo na biyu a karamar hukumar Funtua da ke jihar Katsina.

Shugaban kungiyar kamfen din Masari kuma sakataren gwamnatin jihar, Dr Mustapha Inuwa wadanda ya yi jawabi ga taron manema labarai a jiya Alhamis, 27 ga watan Disamba ya ce tawagar kamfen din za su zagaye dukkanin kananan hukumomi 34 da ke jihar.

Zaben 2019: Gwamna Masari zai kaddamar da kamfen dinsa a gobe
Zaben 2019: Gwamna Masari zai kaddamar da kamfen dinsa a gobe
Asali: Facebook

Ya ce a matsayin su na mambobi masu biyayya ga APC, za su bi dukkanin sharuda da ka’idojin kamfen, inda ya kara da cewa nasarorin da gwamnatin Masari ta samu a kowani bangare na jihar ya isa ya bayar da tabbacin cewa zai yi nasarar yin tazarce.

A cewarsa, za’a kaddamar da dukkaninayyukan da aka kammala a dukka wuraren da za su ziyarta.

KU KARANTA KUMA: Shehu Sani yi martani bayan ikirarin cewa iyalan Buhari na da hannun jari a kamfanoni 2

Ya kuma kara da cewar za kuma su karbi sabbin mambobin siyasa da suka sauya sheka daga sauran jam’iyyun siyasa.

Idan ka na da wata shawara ko bukatar ba mu labari, a tuntube mu a: labaranhausa@corp.legit.ng

Ku same mu a https://www.facebook.com/legitnghausa

Ko a http://twitter.com/legitnghausa

Latsa wannan domin samun sabuwar manhajar labarai ta LEGIT NG Hausa a wayar ku ta hannu: https://play.google.com/store/apps/details?id=com.naij.hausa&hl=en

Shafin NAIJ Hausa ya koma LEGIT

Asali: Legit.ng

Authors:
Mudathir Ishaq avatar

Mudathir Ishaq Mudathir Ishaq is the head of the Hausa desk at Legit.ng. He studied Industrial Chemistry as first degree at the University of Abuja, Journalism (CSR Specialization) with the Michigan State University and runs MSc Industrial Chemistry from the Nasarawa State University, Keffi. With more than a decade experience in news reporting and content editing, he has interviewed influential personalities. He can be reached on: mudathir.ishaq@corp.legit.ng