Da duminsa: Jam'iyyu 5 da zasu kara a muhawara takaran shugaban kasa ranar Juma'a
Kungiyar shirya muhawarar zaben Najeriya NEDG da kungiyar kafofin yada labaran Najeriya BON ta saki sunayen jam'iyyu biyar da zasuyi muhawarar takarar kujeran mataimakin shugaban kasa da na shugaban kasa.
Game da jawabin da sakataren kungiyar, Mr Eddi Emesiri, ya saki, ya ce jam'iyyar Allied Congress Party of Nigeria (ACPN), Alliance for New Nigeria (ANN), All Progressives Congress (APC), Peoples Democratic Party (PDP) da Young Progressives Party (YPP) ne aka zaba.
Za'a gudanar da muhawarar masu takaran kujeran mataimakin shugaban kasa rana Juma'a, 14 ga watan Disamba, 2018 misalin karfe bakwia na yamma a `Transcorp Hilton, kuma za'a gudanar da na shugaban kasa ranan Asabar, 19 ga watan Junairu, 2019.
KU KARANTA: Gobara a babban cocin Katolika
Za'a nuna wannan muhawara a dukkan tashohin Najeriya da kuma a kafofin ra'ayi da sada zumunta.
Wadanda za'ayi muhawarar da su sune:
Farfesa Yemi Osinbajo na jam'iyyar APC
Mr Peter Obi na jam'iyyar PDP
Umma Getso na jam'iyyar YPP
Alhaji Abdulganiyu Galadima na ACPN
Abdullahi Iya na jam'iyyar ANN
Muhimmiyar sanarwa: Shafin NAIJ.com Hausa ya koma LEGIT.ng Hausa. Mun gode da kasancewarku tare da mu.
Latsa wannan domin samun sabuwar manhajar labarai ta Legit.ng Hausa a wayar ku ta hannu: https://play.google.com/store/apps/details?id=ng.legit.hausa&hl=en
Ku biyo mu a shafukanmu na dandalin sada zumunta:
Facebook: https://facebook.com/legitnghausa
Twitter: https://twitter.com/legitnghausa
Idan kuna da wata shawara ko bukatar bamu labari,
Tuntube mu a: labaranhausa@corp.legit.ng
Asali: Legit.ng