Rundunar soji ta tura karin sojoji garin Borno kan rahoton yunkurin kai harin ta’addanci

Rundunar soji ta tura karin sojoji garin Borno kan rahoton yunkurin kai harin ta’addanci

Rundunar sojin Najeriya ta sake tura dakarunta cike da kayan aiki domin su kare Jakana, wani gari a karamar hukumar Konduga da ke jihar Borno.

An gano rundunar wanda aka jona da na Operation Lafiya Dole a ranar Laraba, 5 ga watan Disamba cike da kayayyaki da dabarun yaki a Mainok, wani gari yan mil kadan daga Jakana.

Channels TV ta ruwaito cewa jami’an tsaro sun yada zango kusa da wuraren binciken ababen hawa a yankin inda ake ta bincikar matafiya sosai.

Rundunar soji ta tura karin sojoji gwarin Borno kan rahoton yunkurin kai harin ta’addanci
Rundunar soji ta tura karin sojoji gwarin Borno kan rahoton yunkurin kai harin ta’addanci
Asali: Depositphotos

Hakan baya iya rasa nasaba da wani rahoto da ke yawo tun a ranar Talata na hare-hare da ake kaiwa kauyukan da ke kewaye da Jakana.

KU KARANTA KUMA: Yanzu Yanzu: Majalisar wakilai ta amince da 12 ga watan Yuni a matsayin ranar damokradiyya

Wani dan jarida Ahmed Salkida ya wallafa a shafin twitter cewa “yan ta’addan Boko Haram sun fara taruwa a kauyen Mattari a karamar hukumar Konduga.

“Wajen na kusa da Jakana ko Benishek, akwai hukumomin sojin Najeriya a yankunan biyu, wasu majiyoyi suka ruwaito hakan.”

Sai dai rundunar sojin bata yi martani akan hakan ba tukuna.

Idan ka na da wata shawara ko bukatar ba mu labari, a tuntube mu a: labaranhausa@corp.legit.ng

Ku same mu a https://www.facebook.com/legitnghausa

Ko a http://twitter.com/legitnghausa

Latsa wannan domin samun sabuwar manhajar labarai ta LEGIT NG Hausa a wayar ku ta hannu: https://play.google.com/store/apps/details?id=com.naij.hausa&hl=en

Shafin NAIJ Hausa ya koma LEGIT

Asali: Legit.ng

Online view pixel