An hana kowa yin dawafi sai masu nakasa a Ka'aba

An hana kowa yin dawafi sai masu nakasa a Ka'aba

Rahotanni sun kawo cewa masu kula da Masallatai biyu mafi daraja na kasar Saudiyya sun ware tsawon sa'a biyu inda suka bai wa masu nakasa damar yin dawafi su kadai a ranar Litinin, 3 ga watan Disamba.

Ma'aikatar ta yi hakan ne domin nuna nakasassun a ranar masu nakasa ta duniya wacce ake gudanarwa a ranar 3 ga watan Disamba ta kowace shekara.

Jaridar Saudi Gazette ta ruwaito sakataren ma'aikatar Mashour Al-Monaami, na cewa hakan na nuna yadda Masarautar kasar ke mutunta wadannan mutane a cikin jama’a da kuma ba su hakkokinsu.

An hana kowa yin dawafi sai masu nakasa a Ka'aba
An hana kowa yin dawafi sai masu nakasa a Ka'aba
Asali: UGC

Majalisar Dinkin Duniya ta ware ranar ce domin mayar da hankali kan irin hali da kalubalen da masu nakasa ke ciki a kowane fanni na rayuwa a duniya.

KU KARANTA KUMA: Ya kamata Buhari ya fallasa wadanda su ka nemi kujerar sa tun kafin ya bar Duniya – Shehu Sani

Taken ranar ta bana shi ne: "Tallafawa mutane masu nakasa da kuma da kuma tabbatar da daidato."

Yawanci dai wajen dawafi na yawan cika da mutane ta yadda ko yaushe sai dai masu lalura ko masu nakasa su hau can sama su yi nasu dawafin.

Saudiyya ta kafa wasu dokoki tare da bayar da kulawa ga mutane masu nakasa.

Idan ka na da wata shawara ko bukatar ba mu labari, a tuntube mu a: labaranhausa@corp.legit.ng

Ku same mu a https://www.facebook.com/legitnghausa

Ko a http://twitter.com/legitnghausa

Latsa wannan domin samun sabuwar manhajar labarai ta LEGIT NG Hausa a wayar ku ta hannu: https://play.google.com/store/apps/details?id=com.naij.hausa&hl=en

Shafin NAIJ Hausa ya koma LEGIT

Asali: Legit.ng

Online view pixel