Na roke su (Ja’afar Ja’afar) kada su saki bidiyon amma basu saurareni ba - Kwankwaso (kalli bidiyo)

Na roke su (Ja’afar Ja’afar) kada su saki bidiyon amma basu saurareni ba - Kwankwaso (kalli bidiyo)

Sanata mai wakiltan mazabar Kano ta tsakiya a majalisar dattawan Najeriya, Rabiu Musa Kwankwaso, ya bayyana cewa yana sane da bidiyon da ke nuna gwamnan jihar , Abdullahi Umar Ganduje, yana karban kudi daga hannun yan kwangila.

Ya bayyana cewa ya yi iyakan kokarinsa wajen ganin cewa kada a saki bidiyon nan amma abin bai yiwu ba.

Kana ya bayyana cewa karya akayiwa shugaba Muhammadu Buhari cewa ya karkatar da kudin jihar Kano wajen yakin neman zaben shugaban kasa. Da kuma cewa Ganduje ne ya karasa ayyukan da ya bari.

KU KARANTA: Babbar magana: Na kashe budurwata saboda tana soyayya da yayana - Dan shekaru 16

Kwankwaso, wanda tsohon gwamna ne a jihar Kano, ya bayyana wadannan kalamai ne yayinda yake hira a tashar rediyon Aminchi FM.

Sanata Kwankwaso ya ce ya roki shugaban jaridar yanar gizon, Daily Nigerian, da ya saki bidiyon amma basu sauraresa ba.

Yace: “Ina sane da bidiyon kafin a sakewa duniya ta gani kuma na rokesu kada su saki, amma basu saurareni ba.”

Kalli wani ballin bidiyon jawabinsa:

Sanarwa: Shafin Naij.com Hausa shine yanzu ya koma Legit.ng Hausa, don inganta muku zafafan labarai dama kayatarwa

Latsa wannan domin samun labarai a wayar ku ta hannu: https://play.google.com/store/apps/details?id=com.naij.hausa&hl=en

Ku biyo mu a shafukanmu na dandalin sada zumunta:

Facebook: https://facebook.com/hausa.legit.ng

Twitter: https://twitter.com/hausa.legit.ng

Idan kuna da wata shawara ko bukatar bamu labari,

Tuntube mu a: labaranhausa@corp.legit.com

Asali: Legit.ng

Authors:
Mudathir Ishaq avatar

Mudathir Ishaq Mudathir Ishaq is the head of the Hausa desk at Legit.ng. He studied Industrial Chemistry as first degree at the University of Abuja, Journalism (CSR Specialization) with the Michigan State University and runs MSc Industrial Chemistry from the Nasarawa State University, Keffi. With more than a decade experience in news reporting and content editing, he has interviewed influential personalities. He can be reached on: mudathir.ishaq@corp.legit.ng