Wani ma'aikaci a Kaduna ya rasa aikin sa saboda kaunar Shugaba Buhari
Wani ma'aikaci da gidan yada labarai na Rediyo da Talabijin a jihar Kaduna na DITV-Alheri mallakar tsohon na hannun damar shugaban kasa, Muhammadu Buhari ya rasa aikin sa sakamakon nuna soyayyar shugaba Buhari karara a dandalin sadarwar zamani.
Majiyar mu ta Daily Nigerian ta ruwaito mana cewa shi mai kafar sadarwar zamanin, Mista Baba-Ahmed tsohon na hannun damar shugaban kasa Muhammadu Buhari ne da yayi masa dan sa ido a zaben shekarar 2019 a jam'iyyar APC kafin daga bisani ya sauya sheka zuwa PDP.
Legit.ng Hausa ta samu haka zalika cewa shi ma'aikacin da ya rasa aikin sa mai suna Umar Ridwan, ya zargi cewa saboda ya yada wani rubutu ne a shafin sa na dandalin sadarwar zamani dake da alaka da nuna soyayya ga shugaban.
Sai dai kuma mahukun ta a gidan yada labaran sun musanta zargin nasa inda kuma suka ce sun yi niyyar yanke alaka da shi ne kawai sakamakon damar da kundin tsarin mulki ya tanadar.
Muhimmiyar sanarwa: Shafin NAIJ.com Hausa ya koma legit.ng Hausa. Mun gode da kasancewarku tare da mu.
Latsa wannan domin samun labarai a wayar ku ta hannu: https://play.google.com/store/apps/details?id=com.naij.hausa&hl=en
Ku biyo mu a shafukanmu na dandalin sada zumunta:
Facebook: https://web.facebook.com/legitnghausa?_rdc=1&_rdr
Twitter: https://twitter.com/legitnghausa
Idan kuna da wata shawara ko bukatar bamu labari,
Tuntube mu a: labaranhausa@corp.legit.com
Asali: Legit.ng