Gwamnatin tarayya ta sake kwato Naira biliyan 4, dala miliyan 7 daga hannun barayin gwamnati

Gwamnatin tarayya ta sake kwato Naira biliyan 4, dala miliyan 7 daga hannun barayin gwamnati

Kwamitin nan na musamman da Shugaba Buhari ya kafa domin kwato kadarorin gwamnati dake a hannun ma'aikatan gwamnati ya ce ya samu nasarar kwato akalla Naira biliyan 4, dala miliyan 7 daga hannun barayin gwamnati.

Shugaban kwamitin da aka dorawa alhakin kwato kadarorin, Mista Okoi Obono-Obla shine ya sanar da hakan ga manema labarai a ofishin sa a garin Abuja.

Gwamnatin tarayya ta sake kwato Naira biliyan 4, dala miliyan 7 daga hannun barayin gwamnati
Gwamnatin tarayya ta sake kwato Naira biliyan 4, dala miliyan 7 daga hannun barayin gwamnati
Asali: UGC

KU KARANTA: Daliban jami'ar ABU sun ciri tuta a fannin fasaha

Legit.ng Hausa ta samu kuma cewar sa, kimanin dalar Amurka miliyan 7 ce aka samu a cikin wani asusun ajiya na bankin Heritage da wani tsohon jami'in gwamnati ya boye wadanda kuma kudin na haram ne.

A wani labarin kuma, Shari'ar da Sanata Dino Melaye, Sanatan dake wakiltar mazabar jihar Kogi ta gabas dake a gaban alkalin wata babbar kotun tarayya dake zaman ta a garin Abuja, babban birnin tarayya a unguwar Maitama ta gamu da sabuwar tangarda.

Mun samu cewa alkalin kotun dai ya katse zaman sauraron shari'ar ne a dai dai lokacin da daya daga cikin shaidun masu kara yake bayar da sheda akan tuhumar da ake yi wa Sanatan saboda rashin bin doka wajen gabatar da shi.

Muhimmiyar sanarwa: Shafin NAIJ.com Hausa ya koma legit.ng Hausa. Mun gode da kasancewarku tare da mu.

Latsa wannan domin samun labarai a wayar ku ta hannu: https://play.google.com/store/apps/details?id=com.naij.hausa&hl=en

Ku biyo mu a shafukanmu na dandalin sada zumunta:

Facebook: https://web.facebook.com/legitnghausa?_rdc=1&_rdr

Twitter: https://twitter.com/legitnghausa

Idan kuna da wata shawara ko bukatar bamu labari,

Tuntube mu a: labaranhausa@corp.legit.com

Asali: Legit.ng

Authors:
Mudathir Ishaq avatar

Mudathir Ishaq Mudathir Ishaq is the head of the Hausa desk at Legit.ng. He studied Industrial Chemistry as first degree at the University of Abuja, Journalism (CSR Specialization) with the Michigan State University and runs MSc Industrial Chemistry from the Nasarawa State University, Keffi. With more than a decade experience in news reporting and content editing, he has interviewed influential personalities. He can be reached on: mudathir.ishaq@corp.legit.ng

Online view pixel