El-Rufai ya zabi mace a matsayin abokiyar takara

El-Rufai ya zabi mace a matsayin abokiyar takara

Gwamnan jihar Kaduna, Mallam Nasir El-Rufai ya sanar da zabar Hadiza Balarabe a matsayin abokiyar takararsa a zaben 2019.

A wata sanarwa dauke da sa hannun kakakinsa, Samuel Aruwan, gwamnan ya ce da gan-gan aka zabi Misis Hadiza domin karfafa wa mata gwiwar shiga gwamnati.

Mataimakin gwamna mai ci, Barnabas Bala, ya koma neman kujerar majalisar dokokin kasar kuma tuni ya zamo dan takarar APC a yankin kudancin Kaduna.

El-Rufai ya zabi mace a matsayin abokiyar takara
El-Rufai ya zabi mace a matsayin abokiyar takara
Source: Depositphotos

“Akwai kwamishinoni mata biyar a majalisarsa ta mutane 14, wanda hakan bah aka yake ba gwamnonin da suka fi shi yawan yan majalisa. A tarihin Kaduna wannan ne karo na farko da wata babbar jam’iyyar siyasa ta zabi mace a matsayin abokiyar takara,” cewar sanarwan.

KU KARANTA KUMA: Yanzu Yanzu: WAEC ta gabatar da takardan shaida ga Shugaba Buhari

Misis Hadiza ce babbar sakatariyar hukumar lafiya ta jihar Kaduna a yanzu, matsayin da take rike da shi tun a watan Fabarairun 2016.

Idan ka na da wata shawara ko bukatar ba mu labari, a tuntube mu a: labaranhausa@corp.legit.ng

Ku same mu a https://www.facebook.com/legitnghausa

Ko a http://twitter.com/legitnghausa

Latsa wannan domin samun sabuwar manhajar labarai ta Legit.ng Hausa a wayar ku ta hannu: https://play.google.com/store/apps/details?id=com.naij.hausa&hl=en

Shafin NAIJ.com Hausa ya koma Legit.ng Hausa

Asali: Legit.ng

Authors:
Mudathir Ishaq avatar

Mudathir Ishaq Mudathir Ishaq is the head of the Hausa desk at Legit.ng. He studied Industrial Chemistry as first degree at the University of Abuja, Journalism (CSR Specialization) with the Michigan State University and runs MSc Industrial Chemistry from the Nasarawa State University, Keffi. With more than a decade experience in news reporting and content editing, he has interviewed influential personalities. He can be reached on: mudathir.ishaq@corp.legit.ng