Minti 2 kawai miji na keyi, ku raba mu - Wata mata 'yar Arewa ta roki kotu
Wata matar aure mai suna Hauwa Adamu a ranar Larabar da ta gabata ta roki kotun jiha a unguwar Mararaba, jihar Nasarawa da ta taimaka ta raba auren su da mijin ta domin baya gamsar da ita a rayuwar su ta aure.
Hauwa ta shaidawa kotun dai cewa ita ta gaji da auren na su domin mijin ta iyakar sa mintuna biyu kacal idan suka zo kwanciyar Aure, abun da ta bayyana da cewa yayi mata kadan matuka, zargin da mijin shi kuma ya karyata.

Asali: Depositphotos
KU KARANTA: Yan Luwadi da madigo sun fadi wanda za su zaba a 2019
Legit.ng Hausa ta samu cewa haka zalika Hauwa ta kara da cewa tun lokacin da suka yi aure har yanzu ba ta taba samun ciki ba, lamarin da yake damun ta matuka domin tana son 'ya'ya kuma abun takaici shine yadda mijin na ta ke zargin ta da zubda cikin da dama bata taba samu ba.
Matar dai ta shaidawa kotun cewa ita a shirye take da ta biya mijin kudin sadakin sa da ya bata duk domin ya sauwake mata.
Asali: Legit.ng