'Yan Shi'a sun nemi ganin Buhari akan Sheikh Zakzaky (hotuna)
Akalla tsawon shekara daya kenan da yan kungiyar Musulman Shia ke suntirin yin gangami a babbar birnin tarayya Abuja duk akan bukatar su na neman gwamnatin tarayya ta saki shugaban su Ibrahim El-Zakzaky wanda ke tsare.
Kimanain shekaru uku kenan da aka tsare shugaban nasu tun a watan Disamban 2015 a garin Zariya bayan arangama da yan kungiyar suka yi da tawagar rundunar sojin Najeriya.
Daga bisani salon nasu ya fara sauyawa inda suka fara rubuce-rubuce a manyan allunan talla da kuma jikin gine-ginen gwamnatin na batanci ga Shugaban kasa Muhammadu Buhari da gwamnatinsa.

Asali: Facebook
Kwanakin baya sun je ma'aikatar Sharia suka rufe suna masu fadin ba a yi musu adalci ba. Ko a makonni biyu da suka gabata, dandazon 'yan Shi'a sun nufi fadar Shugaban kasa wato Villa, inda suka dinga ikirarin sai sun je da karfi, suna masu fadin a sake musu Malaminsu.

Asali: Facebook

Asali: Facebook
KU KARANTA KUMA: Yanzu Yanzu: Fayemi ya halarci taron tattalin arziki na kasa yayinda aka nemi Tambuwal da Ahmed aka rasa
A bangaren jami'an tsaro sun hana su shiga sun nemi da su kawo a rubuce cewa suna so su ga Buhari akan Malaminsu. Inda a yau suka rubuta takardar suka mika ga jami'an tsaro da alkawarin za su mika korafin ga shugaba Buhari.
Asali: Legit.ng