Wani dan majalisar wakilai daga Arewa ya sha da kyar a hannun mafusatan matasa

Wani dan majalisar wakilai daga Arewa ya sha da kyar a hannun mafusatan matasa

Wani dan majalisar wakilai a zauren majalisar taraya dake wakiltar mazabar Taura da Ringim a jihar Jigawa dake a shiyyar Arewa maso yammacin Najeriya, Muhammad Gausu Boyi ya sha da kyar a hannun wasu mafusatan matasa.

Kamar yadda muka samu daga majiyoyin mu, lamarin dai ya faru ne a garin Dutse dake zaman babban birnin jihar inda dan majalisar tare da wasu magoya bayan sa suka je domin tantance su a gabanin zabukan fitar da gwani da za'a gudanar.

Wani dan majalisar wakilai daga Arewa ya sha da kyar a hannun mafusatan matasa
Wani dan majalisar wakilai daga Arewa ya sha da kyar a hannun mafusatan matasa
Asali: UGC

Legit.ng ta samu cewa sai dai isar sa farfajiyar tantancewar sai ya gamu da matasa inda suka yi masa ihu tare da fadan kalaman batanci gare shi har ma suka so su buge shi.

Amma dai da taimakon jami'an tsaron dake a wurin, hakan bata samu ba inda aka fita da shi daga wurin har sai da kura ta lafa.

A wani labarin kuma, Shugaban kasar tarayyar Najeriya, Muhammadu Buhari a jiya ya roki malaman addinai a Najeriya da su taimaka ma gwamnatin sa wajen ganin ta yi nasa a yakin da take yi da 'yan ta'addan dake boyewa cikin rigar addini.

Shugaban kasar yayi wannan roko ne a lokacin da ya karbin bakuncin shugabannin kungiyar Qdiriyya ta Afrika a karkashin jagorancin shugaban ta Sheikh Qribullah Nasiru Kabara a fadar sa dake a garin Abuja.

Latsa wannan domin samun labarai a wayar ku ta hannu: https://play.google.com/store/apps/details?id=com.naij.hausa&hl=en

Ku biyo mu a shafukanmu na dandalin sada zumunta:

Facebook: https://facebook.com/naijcomhausa

Twitter: https://twitter.com/naijcomhausa

Idan kuna da wata shawara ko bukatar bamu labari,

Tuntube mu a: labaranhausa@corp.legit.ng

Asali: Legit.ng

Online view pixel