Rikita-Rikita: Gwamnoni 4 na APC sun daura damarar yaki da Oshiomhole

Rikita-Rikita: Gwamnoni 4 na APC sun daura damarar yaki da Oshiomhole

- Gwamnoni 4 na APC sun daura damarar yaki da Oshiomhole

- Gwamnonin sun ce Oshiomhole yana wuce goda da iri

- Gwamnonin sune na Kaduna, Zamfara, Ondo da kuma Ogun

Akalla gwamnoni hudu ne kawo yanzu suka fito fili suka wasa wukar su domin shiga yaki gadan-gadan da shugaban jam'iyya mai mulki ta APC, Kwamared Adams Oshiomhole game da zabukar fitar da gwani da ake yi yanzu haka.

Rikita-Rikita: Gwamnoni 4 na APC sun daura damarar yaki da Oshiomhole
Rikita-Rikita: Gwamnoni 4 na APC sun daura damarar yaki da Oshiomhole
Asali: Depositphotos

KU KARANTA: Dan majalisar tarayya daga Arewa ya sha da kyar a hannun matasa

Gwamnonin da muka samu labarin sun soma yin fito-na-fito da shugaban jam'iyyar dai sune Abdulaziz Yari na jihar Zamfara; Rotimi Akeredolu na jihar Ondo; Nasir El-Rufai daga Kaduna da kuma Ibikunle Amosun daga jihar Ogun.

Legit.ng ta samu cewa gwamnonin dai suna zargin shugaban jam'iyyar ne da wuce makadi da rawa a wajen rawar da ya taka a yayin gudanar da zabukan fitar da gwanin.

Kawo yanzu dai jam'iyyar ta APC ta gudanar da zabukan fitar da gwanin ta na gwamnoni da kuma Sanatoci a mafiya yawan jahohi da kuma mazabun kasar nan.

A wani labarin kuma, Shugaban kasar tarayyar Najeriya a rubutawa majalisar dattawan Najeriya takarda yana neman amincewar su game da wani sabon nadi da yayi a hukumar nan dake yaki da masu yiwa tattalin arzikin kasa zagon kasa watau Economic and Financial Crimes Commission (EFCC) a turance.

Mun samu cewa dai shugaban kasar ya tura sunan Mista Olanipekun Olukoyede a matsayin Sakataren hukumar ta EFCC inda yake neman su tantance shi.

Latsa wannan domin samun labarai a wayar ku ta hannu: https://play.google.com/store/apps/details?id=com.naij.hausa&hl=en

Ku biyo mu a shafukanmu na dandalin sada zumunta:

Facebook: https://facebook.com/naijcomhausa

Twitter: https://twitter.com/naijcomhausa

Idan kuna da wata shawara ko bukatar bamu labari,

Tuntube mu a: labaranhausa@corp.legit.ng

Asali: Legit.ng

Authors:
Mudathir Ishaq avatar

Mudathir Ishaq Mudathir Ishaq is the head of the Hausa desk at Legit.ng. He studied Industrial Chemistry as first degree at the University of Abuja, Journalism (CSR Specialization) with the Michigan State University and runs MSc Industrial Chemistry from the Nasarawa State University, Keffi. With more than a decade experience in news reporting and content editing, he has interviewed influential personalities. He can be reached on: mudathir.ishaq@corp.legit.ng