Zan gyara Najeriya cikin shekaru 2 kacal - Wani dan takarar shugaban kasa

Zan gyara Najeriya cikin shekaru 2 kacal - Wani dan takarar shugaban kasa

- David Mark yace zan gyara Najeriya cikin shekaru 2 kacal

- Ya fadi hakan ne a garin Lokoja

- Yace zai fara ne da farfado tattalin arzikin Najeriya

Daya daga cikin masu neman tikitin takarar shugabancin kasar nan ta Najeriya a zaben 2019 mai zuwa a jam'iyyar adawa ta PDP Sanata David Mark yayi alkawarin gyra Najeriya cikin shekaru biyu kacal idan ya zama shugaban kasa.

Zan gyara Najeriya cikin shekaru 2 kacal - Wani dan takarar shugaban kasa
Zan gyara Najeriya cikin shekaru 2 kacal - Wani dan takarar shugaban kasa
Asali: Facebook

KU KARANTA: An gano inda Nnamdi Kanu ya sulale

Sanata Mark dake zaman tsohon shugaban majalisar dattawan Najeriya yayi wannan ikirarin ne a ranar Talatar da ta gabata a garin Lokoja, babban birnin jihar Kogi lokacin da yake tattaunawa da masu ruwa da tsakin jam'iyyar a jihar.

Legit.ng ta samu cewa fitaccen dan siyasar wanda ya fito daga jihar Benue dake a shiyyar Arewa ta tsakiyar Najeriya ya bayyana cewa cikin shekaru biyu na farkon wa'adin mulkin sa idan ya samu nasarar zama shugaban kasa zai farfado da tattalin arzikin kasar.

A wani labarin kuma, Wani binciken da aka gudanar yana nuni ne da cewa akalla mutane 123 ne suka sayi fom din neman tikitin takarar gwamna a jam'iyyar adawa ta PDP a Najeriya a zaben gama gari da za'a gudanar a shekarar 2019.

Mun samu wadannan alkaluman ne daga wata majiyar mu a babbar hedikwatar jam'iyyar ta PDP dake a garin Abuja bayan da aka sanar da rufe saida fom din a satin da ya gabata.

Latsa wannan domin samun labarai a wayar ku ta hannu: https://play.google.com/store/apps/details?id=com.naij.hausa&hl=en

Ku biyo mu a shafukanmu na dandalin sada zumunta:

Facebook: https://facebook.com/naijcomhausa

Twitter: https://twitter.com/naijcomhausa

Idan kuna da wata shawara ko bukatar bamu labari,

Tuntube mu a: labaranhausa@corp.legit.ng

Asali: Legit.ng

Authors:
Mudathir Ishaq avatar

Mudathir Ishaq Mudathir Ishaq is the head of the Hausa desk at Legit.ng. He studied Industrial Chemistry as first degree at the University of Abuja, Journalism (CSR Specialization) with the Michigan State University and runs MSc Industrial Chemistry from the Nasarawa State University, Keffi. With more than a decade experience in news reporting and content editing, he has interviewed influential personalities. He can be reached on: mudathir.ishaq@corp.legit.ng