Kana da karfin zuciya – PDP ga Dogara yayinda ya dawo jam’iyyar

Kana da karfin zuciya – PDP ga Dogara yayinda ya dawo jam’iyyar

- PDP tayi wa Kakakin majalisa Yakubu Dogara maraba da dawowa tushen sa

- Kwanan nan Dogara ya sauya sheka daga APC zuwa tsohuwar jam’iyyarsa PDP

- PDP ta bayyana dawowar Dogara jam’iyyar a matsayin mataki mai karfin gwiwa

A ranar Lahadi, 16 ga watan Satumba, jam’iyyar Peoples Democratic Party (PDP) tayi wa kakakin majalisar wakilai, Honourable Yakubu Dogara, sannu da zuwa tsohuwar jam’iyyarsa daga All Progressives Congress (APC).

PDP a wata sanarwa dauke da sa hannun sakataren labaranta na kasa, Kola Ologbondiyan, a Abuja ta bayyana cewa dawowar Dogara martani ne ga kiran da jam’iyyar tayiwa masu kishin kasa don su hada kais u ceto kasar.

Ologbodiyan ya bayyana hukuncin Dogara naa sauya sheka daga APC a matsayin yunkuri da ya nuna cewa shi dattijo ne, wadda ke son ganin ci gaban kasar, musamman a wannan lokaci da take cikin mawuyacin hali.

Kana da karfin zuciya – PDP ga Dogara yayinda ya dawo jam’iyyar
Kana da karfin zuciya – PDP ga Dogara yayinda ya dawo jam’iyyar
Asali: UGC

Ya kara da cewa yunkurin Dogara buri ne na al’umman mazabarsa da kuma kiran yan Najeriya dake gangami a karkashin jam’iyyar don ganin PDP ta tsige gwamnatin APC.

KU KARANTA KUMA: Yayan APC sun yi ma gwamnan jahar Zamfara ruwan duwatsu a Gusau

Yace Dogara ya ci gaba da jajircewa wajen tafiyar da harkokin majalisa duk da kokarin karkatar da hankalinsa da jam’iyyar APC ke ta kokarin yi.

Ya bad a tabbacin cewa dawowar Dogara jam’iyyar na alamu ne na cewa PDP zata kafu sannan tayi nasara a jihar Bauchi.

Latsa wannan domin samun labarai a wayar ku ta hannu: https://play.google.com/store/apps/details?id=com.naij.hausa&hl=en

Ku biyo mu a shafukanmu na dandalin sada zumunta:

Facebook: https://facebook.com/naijcomhausa

Twitter: https://twitter.com/naijcomhausa

Idan kuna da wata shawara ko bukatar bamu labari, tuntube mu a: labaranhausa@corp.legit.ng

Asali: Legit.ng

Authors:
Mudathir Ishaq avatar

Mudathir Ishaq Mudathir Ishaq is the head of the Hausa desk at Legit.ng. He studied Industrial Chemistry as first degree at the University of Abuja, Journalism (CSR Specialization) with the Michigan State University and runs MSc Industrial Chemistry from the Nasarawa State University, Keffi. With more than a decade experience in news reporting and content editing, he has interviewed influential personalities. He can be reached on: mudathir.ishaq@corp.legit.ng