Digiri na 3 da Gwamna Ortom ya mallaka na jabu ne – Akume

Digiri na 3 da Gwamna Ortom ya mallaka na jabu ne – Akume

- Sanata George Akume da Gwamna Samuel Ortom sun yi musayar zafafan kalamai

-Akume yace digiri na uku da gwamnan ya mallaka na jabu ne

- Ya kalubalanci Ortom da ya biya ma'aikata da yan fansh bashin alashi da suke bin sa

- Kakakin gwamnan kuma ya bayyana Akume a matsayin mashayi da bai kamata a karbi zancensa ba

Sanata mai wakiltan mazabar arewa maso gabashin Benue, George Akume da Gwamna Samuel Ortom sun yi musayar zafafan kalamai a ranar Litinin, 10 ga watan Satumba.

Akume a wajen taron masu ruwa da tsaki na jam’iyyar All Progressives Congress (APC) da aka gudanar a dakin taron Castle Event Centre, Makurdi a ranar Lahadi, 9 ga watan Satumba ya bayyana Ortom a matsayin mara kokari, tare da zargin cewa gwamnan na dauke da digiri na uku na jabu.

Digiri na 3 da Gwamna Ortom ya mallaka na jabu ne – Akume
Digiri na 3 da Gwamna Ortom ya mallaka na jabu ne – Akume
Asali: Depositphotos

Akume wadda ya zargi gwamnan da tafiyar da shirin zuba jari a al’umma kamar gadon gdansu ya bayyana cewa akwai bukatar a yi waje dashi daga kan kujerar mulki a shekara mai zuwa.

Akume ya kuma zargi Ortom da yawan zagin Shugaban Kasa Muhammadu Buhari.

KU KARANTA KUMA: Rikici ya kunno kai a Jam'iyyar PDP sakamakon wani sabon hukunci da ta yanke

Ya kalubalanci gwamnan da ya biya bashin albashin ma’aikata da nay an fansho da suke bin shi a jihar wadda a cewarsa yunwa na hallaka su.

Amma da yake mayar da martani a madadin ubangidansa, kakakin Ortom, Taav Agerzua ya bayyana Akume a matsayin mashayin da bai kamata a dauki maganarsa da ma’ana ba.

Latsa wannan domin samun sabuwar manhajar labarai ta Legit.ng Hausa a wayarku ta hannu: https://play.google.com/store/apps/details?id=com.naij.hausa&hl=en

Ku biyo mu a shafukan mu na dandalin sada zumunta:

Facebook: https://facebook.com/naijcomhausa

Twitter: https://twitter.com/naijcomhausa

Idan kuna da wata shawara ko bukatar bamu labari, Tuntube mu a: labaranhausa@corp.legit.ng

Asali: Legit.ng

Authors:
Mudathir Ishaq avatar

Mudathir Ishaq Mudathir Ishaq is the head of the Hausa desk at Legit.ng. He studied Industrial Chemistry as first degree at the University of Abuja, Journalism (CSR Specialization) with the Michigan State University and runs MSc Industrial Chemistry from the Nasarawa State University, Keffi. With more than a decade experience in news reporting and content editing, he has interviewed influential personalities. He can be reached on: mudathir.ishaq@corp.legit.ng