Zargin sauya sheka: Ban watsar da yayana ba – Kanin Dankwambo

Zargin sauya sheka: Ban watsar da yayana ba – Kanin Dankwambo

- Buhari Muhammad Dankwambo ya karyata rahoton kafofin watsa labarai na cewa ya yasar da yayansa

- Kanin gwamnan ya kuma kayata cewar ya bar jam'iyyar PDP

- Yace Dankwambon da ake ikirari a kafofin watsa labarai bashi bane

Kanin gwamnan jihar Gombe, Buhari Muhammad Dankwambo ya karyata rahoton kafofin watsa labarai na cewa ya yasar da yayansa, Ibrahim Dankwambo da jam’iyyar PDP.

A wata sanarwa ga manema labarai, kanin Dankwambo ya bayyana rahoton a matsayin mara tushe cewa rade-radi ne kawai.

Ya jadadda cewa yana tare dayayansa cewa shi bai sauya sheka zua jam’iyyar APC kamar yadda ake ta yayatawa.

Zargin sauya sheka: Ban watsar da yayana ba – Kanin Dankwambo
Zargin sauya sheka: Ban watsar da yayana ba – Kanin Dankwambo
Asali: Twitter

Yace gwamnan jihar Gombe uba ne ga dukkanin ahlin gidansu, don haka a zai yi abunda zai bata masa sunansa da martabansa ba.

Ya kara da cewa an kintsa labarin ne don kawai a bata masa suna.

KU KARANTA KUMA: Mune muka haddasa girgizan kasa, mazauna su sa ran ganin wadda yafi na da – Yan asalin Abuja

A bay Legit.ng ta ahoto cewa Buhari Mohammed Dankwambo, jigo a jam'iyyar PDP a jihar Gombe, kuma kanin gwamna Hassan Dankwambo na jihar Gombe ya canja ra'ayinsa kan batun sauya sheka zuwa jam'iyyar APC kamar yadda ya fadi a ranar Laraba 5 ga watan Satumban 2018.

An tattaro cewa Buhari Dankwambo ya yanke shawarar cigaba da kasancewa a jam'iyyar PDP ne bayan ya yi shawara da 'yan uwansa da kuma sauran aminansa na siyasa.

Idan ka na da wata shawara ko bukatar ba mu labari, a tuntube mu a labaranhausa@corp.legit.ng

Ku same mu a https://www.facebook.com/naijcomhausa

Ko a http://twitter.com/naijcomhausa

Latsa wannan domin samun sabuwar manhajar labarai ta Legit.ng Hausa a wayar ku ta hannu: https://play.google.com/store/apps/details?id=com.naij.hausa&hl=en

Asali: Legit.ng

Authors:
Mudathir Ishaq avatar

Mudathir Ishaq Mudathir Ishaq is the head of the Hausa desk at Legit.ng. He studied Industrial Chemistry as first degree at the University of Abuja, Journalism (CSR Specialization) with the Michigan State University and runs MSc Industrial Chemistry from the Nasarawa State University, Keffi. With more than a decade experience in news reporting and content editing, he has interviewed influential personalities. He can be reached on: mudathir.ishaq@corp.legit.ng