Yanzu Yanzu: Boko Haram sun sake kai sabon hari sansanin sojoji a Borno

Yanzu Yanzu: Boko Haram sun sake kai sabon hari sansanin sojoji a Borno

- Boko Haram sun sake kai sabon hari a sansanin sojoji dake Baga, jihar Borno

- Harin ya afku ne kasa da sa'o'i 24 bayan sun kai mamaye yankin Gudumbali dake karamar hukumar Guzamala a jihar

Yan ta’addan Boko Haram sun sake kai sabon hari a sansanin sojoji dake Baga a karamar hukumar Kukawa dake jihar Borno, kwana daya bayan sun mamaye yankin Gudumbali dake karamar hukumar Guzamala sannan suka kori mazauna yankin, jaridar Vanguard ta ruwaito.

Rundunar sojin Najeriya a ranar Lahadi, 9 ga watan Satumba ta tabbatar da wani harin ta’addanci a Gudumbali, cewa dakarunta na sashi 82 da na bataliya 158 sun dakile harin sannan suka dawo da zaman lafiya a yankin.

Daraktan labarai na rundunar sojin, Birgediya Janar Texas Chukwu yace yan ta’addan sun cinna ma wasu gine-gine wuta a garin amma babu wadda a rasa ransa.

Yanzu Yanzu: Boko Haram sun sake kai sabon hari sansanin sojoji a Borno
Yanzu Yanzu: Boko Haram sun sake kai sabon hari sansanin sojoji a Borno
Asali: Facebook

Majiyarmu ta rahoto cewa a ranar Asabar yan ta’addan Boko Haram sun shigi dakarun soji a Gudumbali sannan suka yasar da mazauna yankin zuwa garin Gubio.

KU KARANTA KUMA: Ba na gudun ayi amfani da na’u’rorin zamani a zaben 2019 – Shugaban kasa Buhari

Idanun saida sun bayyana cewa yan ta’addan sun kama garin bayan sun shiga yankin cikin adadi masu yawa sannan suka fara harbe-harbe wadda hakan yasa subban mazauna yankin tserewa.

An tattaro cewa bayan harin da suka kai Gudumbali, yan ta’addan sun koma Baga a karamar hukumar Kukawa inda suka sake kai wani harin a sansanin sojoji, inda ba’a san adadin mutanen da suka mutu a wuraren biyu ba adaidai lokacin wannan rahoton.

Vanguard ta rahoto cewa Ahmed Salkida, dan jaridar dake da kusanci da yan ta’adda ya bayyana a shafin twitter cewa yan ta’addan na da wani boyayyen kudirin tunda suke ta kai hare-hare sansanin sojoji akai–akai.

Idan ka na da wata shawara ko bukatar ba mu labari, a tuntube mu a labaranhausa@corp.legit.ng

Ku same mu a https://www.facebook.com/naijcomhausa

Ko a http://twitter.com/naijcomhausa

Latsa wannan domin samun sabuwar manhajar labarai ta Legit.ng Hausa a wayar ku ta hannu: https://play.google.com/store/apps/details?id=com.naij.hausa&hl=en

Asali: Legit.ng

Authors:
Mudathir Ishaq avatar

Mudathir Ishaq Mudathir Ishaq is the head of the Hausa desk at Legit.ng. He studied Industrial Chemistry as first degree at the University of Abuja, Journalism (CSR Specialization) with the Michigan State University and runs MSc Industrial Chemistry from the Nasarawa State University, Keffi. With more than a decade experience in news reporting and content editing, he has interviewed influential personalities. He can be reached on: mudathir.ishaq@corp.legit.ng