Tsugene bata kare ba: Sanata Shehu Sani da wasu manyan 'yan APC sun kai kara gaban uwar jam'iyya

Tsugene bata kare ba: Sanata Shehu Sani da wasu manyan 'yan APC sun kai kara gaban uwar jam'iyya

- Sanata Shehu Sani da wasu manyan 'yan APC sun kai kara gaban uwar jam'iyya

- Yace shi da su duka basu yadda da zaben fitar da gwani na deliget ba

- Yace cin hanci da rashawa ne kawai tattare da hakan

Fitaccen dan majalisar dattawan Najeriya dake wakiltar mazabar Kaduna ta tsakiya, Sanata Shehu Sani a ranar Talatar da ta gabata ya jagoranci wasu 'yan jam'iyyar APC zuwa hedikwatar ta kai kara.

Tsugene bata kare ba: Sanata Shehu Sani da wasu manyan 'yan APC sun kai kara gaban uwar jam'iyya
Tsugene bata kare ba: Sanata Shehu Sani da wasu manyan 'yan APC sun kai kara gaban uwar jam'iyya
Asali: Twitter

KU KARANTA: Kwankwaso ya kwace PDP a jihar Kano

Kamar dai yadda muka samu, Sanata Shehu Sani da sauran 'yan APC sun je ne a wajen uwar jam'iyyar inda suka bukaci cewa ta tilastawa jam'iyyar a matakin jihar ta Kaduna gudanar da zabukan fitar da gwani na tsarin kato-bayan-kato.

Legit.ng ta samu cewa a lokacin da suke yi wa manema labarai jawabi a wajen kai takardar karar, sun bayyana cewa ya kamata jam'iyyar ta sa baki don ganin an kori cin hancin da kan dabaibaye tsarin zabukan fitar da gwani na 'yan takara a zabukan 2019 masu zuwa.

Mai karatu dai zai iya tuna cewa a satukan da suka gabata ne dai kwamitin zartaswa na jam'iyyar ya fitar da tsarin gudanar da zabukan fitar da gwani na kato-bayan-kato inda kuma wasu gwamnoni suka nuna rashin amincewar su da hakan.

A wani labarin kuma, Daya daga cikin manyan malaman addinan kirista a kasar nan kuma shugaban rukunin majami'un Mount Zion Faith Global Liberation Ministry Inc.( a.k.a. By Fire By Fire) da ke a garin Nnewi, jihar Anambra mai suna Bishop Abraham Udeh ya yi kaca-kaca da masoya Muhammadu Buhari.

Bishop din wanda a jiya ya zanta da manema labarai, ya bayyana cewa dukkan masu son Shugaban kasar Muhammadu Buhari ya zarce to lallai shi babban makiyin demokradiyya ne.

Latsa wannan domin samun labarai a wayar ku ta hannu: https://play.google.com/store/apps/details?id=com.naij.hausa&hl=en

Ku biyo mu a shafukanmu na dandalin sada zumunta:

Facebook: https://facebook.com/naijcomhausa

Twitter: https://twitter.com/naijcomhausa

Idan kuna da wata shawara ko bukatar bamu labari,

Tuntube mu a: labaranhausa@corp.legit.ng

Asali: Legit.ng

Authors:
Mudathir Ishaq avatar

Mudathir Ishaq Mudathir Ishaq is the head of the Hausa desk at Legit.ng. He studied Industrial Chemistry as first degree at the University of Abuja, Journalism (CSR Specialization) with the Michigan State University and runs MSc Industrial Chemistry from the Nasarawa State University, Keffi. With more than a decade experience in news reporting and content editing, he has interviewed influential personalities. He can be reached on: mudathir.ishaq@corp.legit.ng