Zan kashe kaina idan Buhari ya fadi a zaben 2019 – Wani mutumin Abuja yayi barazana

Zan kashe kaina idan Buhari ya fadi a zaben 2019 – Wani mutumin Abuja yayi barazana

- Wani dan Najeriya yayi barazanar kashe kansa idan har Shugaba Buhari bai lashe zaben 2019 ba

- An gano mutumin tsaye a mararraba a Abuja rike da babban kwalin sanarwar dakedauke da rubutu akan hakan

- Shugaba Buhari na neman tazarce a jam’iyyar APC

Wani mutimin Najeriya ya sha alwashin kashe kansa idan har Shugaban kasa Muhammadu Buhari bai yi nasara a zaben 2019.

Wakilin Legit.ng na yankin, Kingsley okezie ya rahoto cewa mutumin ya haifar da karamin kwaikwayo a wani gari dake Abuja lokacin da ya fito unguwanni domin yin wannan furucin.

An gano mutumin tsaye a mararraba a Abuja rike da babban kwalin sanarwa inda ya rubuta “Idan Muhammad Buhari bai ci zaben 2019 ba, zan kashe kaina”, kamar yadda yake rubuce akai.

Zan kashe kaina idan Buhari ya fadi a zaben 2019 – Wani mutumin Abuja yayi barazana
Zan kashe kaina idan Buhari ya fadi a zaben 2019 – Wani mutumin Abuja yayi barazana
Asali: Depositphotos

A halin da ake ciki, mun ji cewa ayyuka sun kachame a babban sakatariyar jam’iyyar Democratic Party (PDP) dake Abuja a jiya, Talata, 28 ga watan Agusta yayinda jam’iyyar ta fara siyar da fam din ra’ayi tsayawa tkara ga yan siyasar dake son takara a zaben 2019 a inuwarta.

Yayin da yan takara da dama suka biya kudin fam a asusun banki, wasu sun biya ne ta na’urar POS.

KU KARANTA KUMA: Haramci akan kodin da tramadol ya sanya ayyuka mutane 25,000 cikin hatsari – Kungiya

Daga cikin wadanda suka yanki fam din a jiya sun hada da Gwamnan jihar ombe,Ibrahim Dankwambo, wanda ke neman takarar kujerar shugabancin kasa a karkshn PDP a zaben 2019.

Bayan Dankwambo, tsohon gwamnan jihar Jigawa, Sule Lamido ma ya yaki fam din taarar shugabancin kasa a jam’iyyara jiya. Dukkansu su biyun sun biya naira miliyan biyu na nuna ra’ayi da kuma naira mliyan 10 na fam din.

Latsa wannan domin samun labarai a wayar ku ta hannu: https://play.google.com/store/apps/details?id=com.naij.hausa&hl=en

Ku biyo mu a shafukanmu na dandalin sada zumunta:

Facebook: https://facebook.com/naijcomhausa

Twitter: https://twitter.com/naijcomhausa

Idan kuna da wata shawara ko bukatar bamu labari, tuntube mu a: labaranhausa@corp.legit.ng

Asali: Legit.ng

Online view pixel