Mutane 24 ke gadin Hajr-el-Aswad a Harami, shin me yasa?

Mutane 24 ke gadin Hajr-el-Aswad a Harami, shin me yasa?

Hajarul Aswad: Ma’anar wannan kalma a harshen Hausa shine ‘bakin dutse’. Wannan dutse na ajiye a gabashin jikin Ka’abah a harami. Ana daukn wannan dutse da matukar muhimmanci a addinin Musulunci. Shine dutsen da Allah ﷻ ya turowa manzo Ibrahim ﷺ daga sama.

Alakar annabi Ibrahim da Hajarul aswad: Allah ya umurci manzonsa Ibrahim ya sanya dutsen mai albarka a wani lungun Ka’aba. Daga bakin dutsen aka fara Tawafi kuma nan ake tsayawa.

Mahajjata da masu gabatar da Umrah na sumbatan dutsen a matsayin Ibadah saboda manzon Allah ﷺ da sahabbansa sun yi wannan abu.

Mutane 24 ke gadin Hajr-el-Aswad a Harami, shin me yasa
Mutane 24 ke gadin Hajr-el-Aswad a Harami, shin me yasa

Dutsen ya taba fashewa: A da, dutsen guda daya ne babba, amma bisa ga wasu rikice-rikicen tarihin da ya faru, an fasa dutsen zuwa balli 8. An tattara Wannan balli takwas cikin qwaryan azurfa domin hanashi sake fashewa.

A shekarar 930, mayakan Al-Karmati sun sace Hajarul Aswad, suka hallaka jama’a a harami kuma suka jefa gawawwakinsu cikin rijiyan Zam-Zam.

Sai a shekarar 952 ne aka samu daman dawo da Hajarul Aswad. Tun daga lokacin aka sanya masu gadi na musamman domin kula da dutsen a koda yaushe.

KU KARANTA: Wannan Amarya ta rasu a daren ranan aurenta

Jami’an tsaro 24 ke tsaron Hajarul Aswad a ranan daya. Kowanne daga cikinsu zai tsaya a wajen na tsawon sa’a daya.

Latsa wannan domin samun labarai a wayar ku ta hannu: https://play.google.com/store/apps/details?id=com.naij.hausa&hl=en

Ku biyo mu a shafukanmu na dandalin sada zumunta:

Facebook: https://facebook.com/naijcomhausa

Twitter: https://twitter.com/naijcomhausa

Idan kuna da wata shawara ko bukatar bamu labari,

Tuntube mu a: labaranhausa@corp.legit.ng

Asali: Legit.ng

Authors:
Mudathir Ishaq avatar

Mudathir Ishaq Mudathir Ishaq is the head of the Hausa desk at Legit.ng. He studied Industrial Chemistry as first degree at the University of Abuja, Journalism (CSR Specialization) with the Michigan State University and runs MSc Industrial Chemistry from the Nasarawa State University, Keffi. With more than a decade experience in news reporting and content editing, he has interviewed influential personalities. He can be reached on: mudathir.ishaq@corp.legit.ng