Mutane 24 ke gadin Hajr-el-Aswad a Harami, shin me yasa?

Mutane 24 ke gadin Hajr-el-Aswad a Harami, shin me yasa?

Hajarul Aswad: Ma’anar wannan kalma a harshen Hausa shine ‘bakin dutse’. Wannan dutse na ajiye a gabashin jikin Ka’abah a harami. Ana daukn wannan dutse da matukar muhimmanci a addinin Musulunci. Shine dutsen da Allah ﷻ ya turowa manzo Ibrahim ﷺ daga sama.

Alakar annabi Ibrahim da Hajarul aswad: Allah ya umurci manzonsa Ibrahim ya sanya dutsen mai albarka a wani lungun Ka’aba. Daga bakin dutsen aka fara Tawafi kuma nan ake tsayawa.

Mahajjata da masu gabatar da Umrah na sumbatan dutsen a matsayin Ibadah saboda manzon Allah ﷺ da sahabbansa sun yi wannan abu.

Mutane 24 ke gadin Hajr-el-Aswad a Harami, shin me yasa
Mutane 24 ke gadin Hajr-el-Aswad a Harami, shin me yasa

Dutsen ya taba fashewa: A da, dutsen guda daya ne babba, amma bisa ga wasu rikice-rikicen tarihin da ya faru, an fasa dutsen zuwa balli 8. An tattara Wannan balli takwas cikin qwaryan azurfa domin hanashi sake fashewa.

A shekarar 930, mayakan Al-Karmati sun sace Hajarul Aswad, suka hallaka jama’a a harami kuma suka jefa gawawwakinsu cikin rijiyan Zam-Zam.

Sai a shekarar 952 ne aka samu daman dawo da Hajarul Aswad. Tun daga lokacin aka sanya masu gadi na musamman domin kula da dutsen a koda yaushe.

KU KARANTA: Wannan Amarya ta rasu a daren ranan aurenta

Jami’an tsaro 24 ke tsaron Hajarul Aswad a ranan daya. Kowanne daga cikinsu zai tsaya a wajen na tsawon sa’a daya.

Latsa wannan domin samun labarai a wayar ku ta hannu: https://play.google.com/store/apps/details?id=com.naij.hausa&hl=en

Ku biyo mu a shafukanmu na dandalin sada zumunta:

Facebook: https://facebook.com/naijcomhausa

Twitter: https://twitter.com/naijcomhausa

Idan kuna da wata shawara ko bukatar bamu labari,

Tuntube mu a: labaranhausa@corp.legit.ng

Asali: Legit.ng

Online view pixel