An kama mutane 5 akan kisan jami’an yan sanda 7 da aka yi a Abuja

An kama mutane 5 akan kisan jami’an yan sanda 7 da aka yi a Abuja

Kwanaki biyar bayan kisan da aka yiwa jami’an yan sanda biyar a Abuja, yan sanda sun ce sun kama mutane biyar da ake zargi da hannu a harin.

An tattaro cewaa tawagar bincike na kokarin kama sauran mutanen da suka gudu akan lamarin.

Jami’in hulda da jama’a narundunar yan sandan, Mukaddashin DCP Jimoh Moshood yayi bayanin cewa ana cigaba da bincike domin gurfanar da sauran mutanen dake da hannu a kisan jami’an yan sandan.

An kama mutane 5 akan kisan jami’an yan sanda 7 da aka yi a Abuja
An kama mutane 5 akan kisan jami’an yan sanda 7 da aka yi a Abuja

An harbe jami’an wadanda ke aiki na musamman a babban birnin tarayya a ranar Litinin da daddare a shataletalen Galaimawa, Abuja sannan kuma naka sace makamansu.

KU KARANTA KUMA: Ina da digiri a fannin hada magunguna da digiri na 2 a fannin tsarin lafiya amma na zabi aikin gyaran jiki domin dogaro da kai - Matashiya

Da yake Karin bayani kan binciken a ranar Juma’a, Moshood ya ce sufeto janar nay an sanda, Ibrahim Idris, ya yi umurnin cewa a biya dukka alawus din wadanda abun ya shag a iyalansu.

Idan ka na da wata shawara ko bukatar ba mu labari, a tuntube mu a labaranhausa@corp.legit.ng

Ku same mu a https://www.facebook.com/naijcomhausa

Ko a http://twitter.com/naijcomhausa

Latsa wannan domin samun sabuwar manhajar labarai ta Legit.ng Hausa a wayar ku ta hannu: https://play.google.com/store/apps/details?id=com.naij.hausa&hl=en

Asali: Legit.ng

Online view pixel