Yanzu-yanzu: Buhari ya tafi kasar Mauritania

Yanzu-yanzu: Buhari ya tafi kasar Mauritania

- Shugaba Muhammadu Buhari ya tafi kasar Mauritania

- Zai yi kwana biyu a taron inda zai gabatar da jawabi

Labarin da ke shigowa yanzu na nuna cewa jirgin shugaba Muhammadu Buhari ya tashi yanzu a babban filin jirgin saman Umaru Musa Yar'adua da ke jihar Katsina zua kasar Mauritania domin halartan taron gamayyar kasashen Afrika wato AU na 31 ranan 1 da 2 ga watan Yuli, 2018.

Yanzu-yanzu: Buhari ya tafi kasar Mauritania
Yanzu-yanzu: Buhari ya tafi kasar Mauritania

Taron na wannan shekaran dai na ke take : “Samun nasara kan yaki da rashawa: Yadda za’a kawo sauyi nahiyar Afrika”. Shugaba Muhammadu Buhari ne zai gabatar da jawabi na musamman akan wannan take.

Yanzu-yanzu: Buhari ya tafi kasar Mauritania
Yanzu-yanzu: Buhari ya tafi kasar Mauritania

Sannan shugaban gamayyar kasashen Afrikan kuma shugaban kasan Ruwanda, Paul Kagama, zai gabatar da jawabi kan sauye-sauyen gamayyar, shi kuma shugaban kasan Nijar, Mahamadou Issoufou, zai gabatar da nasa kan kasuwanci a Afirka.

Wannan shi ne karo na farko da za’a yi taron a kasar Mauritania tun bayan kafa ta.

Yanzu-yanzu: Buhari ya tafi kasar Mauritania
Yanzu-yanzu: Buhari ya tafi kasar Mauritania

Latsa wannan domin samun labarai a wayar ku ta hannu: https://play.google.com/store/apps/details?id=com.naij.hausa&hl=en

Ku biyo mu a shafukanmu na dandalin sada zumunta:

Facebook: https://facebook.com/naijcomhausa

Twitter: https://twitter.com/naijcomhausa

Idan kuna da wata shawara ko bukatar bamu labari,

Tuntube mu a: labaranhausa@corp.legit.ng

Asali: Legit.ng

Online view pixel