Zargin kashe Mijinta: Shari’ar Maryam Sanda ta samu tasgaro a babbar Kotun Abuja

Zargin kashe Mijinta: Shari’ar Maryam Sanda ta samu tasgaro a babbar Kotun Abuja

Shari’a da aka shigar da Maryam Sanda, matar da ake zargi da yi ma Mijinta kisan gilla, Bilyaminu Bello, ta samu akasi sakamakon rashin lafiyar lauya mai shigar da kara, James Idachaba, kamar yadda kamfanin dillancin labaru, NAN, ta ruwaito.

Majiyar Legit.ng ta ruwaito ana tuhumar Maryam Sanda da halaka mijinta a ranar 19 ga watan Nuwambar shekarar 2017, ta hanyar caccaka masa wuka, tare da wasu mutane guda uku da suka hada da mahaifiyarta, Maimuna Aliyu, kaninta Aliyu da yar aikinta Sadiya Aminu.

KU KARANTA: An gurfanar Matar da ta kekketa Uwardakinta da Reza gaban Kuliya manta sabo

Shi dai Bilyaminu da yake ga tsohon shugaban jam’iyyar PDP, tsohon Minista kuma tsohon shugaban hukumar Kwastam, Dakta Halliru Bello Mohammed, inda a zaman kotun na ranar Alhamis, 27 ga watan Yuni, lauya mai kara ya nemi a dage sauraron karar saboda bashi da lafiya.

Zargin kashe Mijinta: Shari’ar Maryam Sanda ta samu tasgaro a babbar Kotun Abuja
Shari’ar Maryam Sanda a Kotu

“Ya mai shari’a, bani da lafiya matuka, kuma ina bukatar samun kulawa a Asibiti, da kyar na kawo kaina Kotun nan saboda tsananin ciwo da nake fama da shi, idan aka lura har shaidanmu yazo gaban Kotu don nuna muhimmancin da muke baiwa wannan shari’a, don haka nake rokon Kotu ta dage karar.” Inji lauya Idachaba.

Bayan sauraron bukatar lauya mai kara, Alklin Kotun, Mai sharia Yusuf Halilu ya dage sauraron karar zuwa ranar 4 ga watan Oktoba, wannan ba shi ne dage sauraron karar na farko ba, inda a baya ma sai da lauyan Maryam, Joseph Daudu ya nemi a dage karar zuwa ranar 15 ga watan Mayu.

Ku biyo mu a https://www.facebook.com/naijcomhausa

ko a http://twitter.com/naijcomhausa

KU LATSA: Hanyar sauko da sabuwar manhajar jaridar Legit.ng Hausa cikin sauki

Ga masu shawara ko korafi, a same mu a labaranhausa@corp.legit.ng

Asali: Legit.ng

Online view pixel