Musulunci zai iya mamaye Najeriya kafin shekarar 2043 - Inji wata kungiyar Kiristoci

Musulunci zai iya mamaye Najeriya kafin shekarar 2043 - Inji wata kungiyar Kiristoci

"Addinin Kiristanci zai bacewa daga doron kasar Najeriya zuwa 2043"

Musulunci zai iya mamaye Najeriya kafin shekarar 2043 - Inji wata kungiyar Kiristoci

Wata kungiyar kiristoci a Najeriya karkashin jagorancin tsohon ministan tsaron Najeriya Laftanal Janar Theophilus Danjuma, Solomon Asemota mai suna National Christian Elders Forum, NCEF tayi hasashen cewa addinin kiristanci zai shafe daga Najeriya kafin shekarar 2043.

Musulunci zai iya mamaye Najeriya kafin shekarar 2043 - Inji wata kungiyar Kiristoci
Musulunci zai iya mamaye Najeriya kafin shekarar 2043 - Inji wata kungiyar Kiristoci

KU KARANTA: Matsaloli 5 da ke hana 'yan mata samun miji a kasar Hausa

Kungiyar ta yi wannan hasashen ne a cikin wata makala da ta gabatar a yayin wani taron kiristocin a garin Legas inda ta bayyana tsoron ta da cewa addinin muslunci tuni ya kama hanyar mamaye kasar.

Legit.ng ta samu cewa sai dai kungiyar ta NCEF ta dora alhakin wannan barazanar da addinin kiristan ke fuskanta da rashin katabus din da hadakar kungiyar kiristocin ta CAN ke yi wajen ganin ta hada kan dukkan kiristocin Najeriya.

Daga karshe kuma kungiyar ta National Christian Elders Forum ta bukaci da a rushe kungiyar CAN sannan kuma a sake mata fasali da wuri kafin zabukan shekarar 2019.

Latsa wannan domin samun labarai a wayar ku ta hannu: https://play.google.com/store/apps/details?id=com.naij.hausa&hl=en

Ku biyo mu a shafukanmu na dandalin sada zumunta:

Facebook: https://facebook.com/naijcomhausa

Twitter: https://twitter.com/naijcomhausa

Idan kuna da wata shawara ko bukatar bamu labari,

Tuntube mu a: labaranhausa@corp.legit.ng

Asali: Legit.ng

Online view pixel