Arziki-kashi: Zahara Buhari ta tafi kasar Sifaniya hutun haihuwa

Arziki-kashi: Zahara Buhari ta tafi kasar Sifaniya hutun haihuwa

Wani rahoton da muke samu daga majiyoyin mu na nuni ne da cewa diyar shugaban kasa kuma matar dan mashahurin mai kudin nan Ahmad Ndimi watau Zahara Buhari tuni ta nufi kasar Sifaniya dake a Nahiyar turai inda ake saran acanne zata haihu.

Majiyar mu dai ta ambato cewa Zahara din dai ta shafe kwanki da dama a kasar ta Sifaniya tare da angon ta inda suke zaune a wani gidan surikin ta, mahaifin mijinta.

Arziki-kashi: Zahara Buhari ta tafi kasar Sifaniya hutun haihuwa
Arziki-kashi: Zahara Buhari ta tafi kasar Sifaniya hutun haihuwa

KU KARANTA: Kotun tarayya ta hana Shekarau zuwa Umarah

Legit.ng ta samu cewa nan bada jimawaba ba ne dai ake saran Zahara zata haihu.

A kwanan baya ne dai muka ruwaito maku cewa Zahra Buhari din ta samu juna biyu wanda har ya bayyana a cikin wani hoto da aka dauka a wajen bikin diyar Dangote, Fatima da angon ta Abubakar.

Muna fatan Allah ya sauke ta lafiya.

Idan ka na da wani shawara ko bukatan bamu labari, tuntube mu a labaranhausa@corp.legit.ng Ku ci gaba da bin mu a Facebook: https://www.facebook.com/naijcomhausa da

Kuma Tuwita: http://twitter.com/naijcomhausa

KU LATSA: Sabuwar hanyar karanta labarain Legit.ng HAUSA

https://play.google.com/store/apps/details?id=com.naij.hausa&hl=en

Asali: Legit.ng

Online view pixel