Tarihi: Yakokin Musulunci 4 da akayi cikin watan Ramadan

Tarihi: Yakokin Musulunci 4 da akayi cikin watan Ramadan

Da yawa daga cikin Musulmai basu san an yi yakoki da dama cikin watan Ramadana a zamanin sahabbai da wadanda suka biyo bayansu.

Daga yakin Fatahu Makkah zuwa yarjejeniya Baqt, da kuma yakin Badar. Amma a yau, jaridar Legit.ng zata kawo muku yakoka 4 wadanda Musulmai suka samu gagarumin nasara a cikin watan Ramadana.

1- Yakin Badar: Yakin da yafi shahara kuma yaki na faro da Musulmai sukayi a tarihi ya faru ne a watan Ramadana, shekara 2 bayan Hijran manzon Allah ﷺ daga Makkah zuwa Madina.

2-Yakin Tabuk 8 AH: Duk da cewan ba’ayi fito na fito ba wannan yaki, Musulmai sun samu gagarumin nasara yayinda rundunar 30,000 karkashin jagorancin manzon Allah ﷺ suka tafi yakan Romawa.

Amma da suka isa, aboka adawa sunyi kasa a guiwa basu fito filin daga ba.

3- Yakin Ain Jalut: An yi wannan yaki ne shekara 658 bayan hijra inda sojin Musulmi suka karfin Mongolawa da sukayi kokarin lalata kasashen Musulmai. Miliyoyin Muslmai sunyi shahada a wannan yaki.

4-Yakin Hattin: An yi wannan yaki ne a shekarar 583 bayan hijra yayinda arnan suka yai kasashen Musulmai kuma suka kwace Kudus. Bayan yakin Hattin, musulmai karkashin jagorancin Salahuddenil Ayyubi suka kwato Kudus.

Latsa wannan domin samun labarai a wayar ku ta hannu: https://play.google.com/store/apps/details?id=com.naij.hausa&hl=en

Ku biyo mu a shafukanmu na dandalin sada zumunta:

Facebook: https://facebook.com/naijcomhausa

Twitter: https://twitter.com/naijcomhausa

Idan kuna da wata shawara ko bukatar bamu labari,

Tuntube mu a: labaranhausa@corp.legit.ng

Asali: Legit.ng

Authors:
Mudathir Ishaq avatar

Mudathir Ishaq Mudathir Ishaq is the head of the Hausa desk at Legit.ng. He studied Industrial Chemistry as first degree at the University of Abuja, Journalism (CSR Specialization) with the Michigan State University and runs MSc Industrial Chemistry from the Nasarawa State University, Keffi. With more than a decade experience in news reporting and content editing, he has interviewed influential personalities. He can be reached on: mudathir.ishaq@corp.legit.ng