Karshen zamani: Dalibi dan aji 1 a karamar Sakandare ya rubutawa malamar sa wasikar soyayya

Karshen zamani: Dalibi dan aji 1 a karamar Sakandare ya rubutawa malamar sa wasikar soyayya

A wani lamari da ya auku da ke kama da almara a Najeriya, mun samu cewa wani dalibi dan aji daya a karamar Sakandare ya rubutawa malamar sa wasikar soyayya inda ya bayyana mata yadda yake matukar kaunar ta.

Malamar dai mai suna Chioma U. Jane ta cika da mamaki da samun wannan wasika inda batayi wata-wata ba ta bayyana wa abokan ta lamarin kafin daga bisani maganar tayi ta yawo a kafafen sadarwar zamin.

Karshen zamani: Dalibi dan aji 1 a karamar Sakandare ya rubutawa malamar sa wasikar soyayya
Karshen zamani: Dalibi dan aji 1 a karamar Sakandare ya rubutawa malamar sa wasikar soyayya

Legit.ng ta samu cewa dai dalibin a cikin wasikar sa ya dauki dogon lokaci yana bayyana mata yadda take da matukar kyau tare da yi masa kwarjini a ido a duk lokacin da ya kalle ta.

Haka kuma dalibin ya roki malamar da ta amince da soyayyar sa domin a cewar sa, yana ji a ran sa zai yi kudi a nan gaba kuma yana da niyyar auren ta in har ta amince masa.

Idan ka na da wani shawara ko bukatan bamu labari, tuntube mu a labaranhausa@corp.legit.ng Ku ci gaba da bin mu a Facebook: https://www.facebook.com/naijcomhausa da

Kuma Tuwita: http://twitter.com/naijcomhausa

KU LATSA: Sabuwar hanyar karanta labarain Legit.ng HAUSA

https://play.google.com/store/apps/details?id=com.naij.hausa&hl=en

Asali: Legit.ng

Online view pixel