Gidan Shi’a ya barke: Bangare daya sun nuna goyon bayansu ga gwamnati

Gidan Shi’a ya barke: Bangare daya sun nuna goyon bayansu ga gwamnati

Wani bangaren kungiyar Shi’a mai suna Rasulul A’azam Foundation, RAAF, a ranan asabar ta nuna goyon bayanta ga gwamnatin Najeriya sabanin bangaren Ibrahim Zakzaky masu fito na fito da gwamnati.

Sakataren kungiyar Rasulul A’azam Foundation, RAAF, Sale Zaria ya bayyana hakan ne a wata hira da manema labarai a taron bikin tunawa da Imam El Mahdi da sukayi karamar hukumar Ngoggo da ke jihar Kano.

Game da cewarsa, Rasulul A’azam Foundation, RAAF, yan zaman lafiya ne, masu zaman kansu kuma masu son hadin kan Najeriya.

Gidan Shi’a ya barke: Bangare daya sun nuna goyon bayansu ga gwamnati
Gidan Shi’a ya barke: Bangare daya sun nuna goyon bayansu ga gwamnati

Mal Sale Zaria ya yi kira ga Musulmai da mutanen Najeriya da su nisanta kansu da duk wani abu da zai tada rikicin addini da kabila a Najeriya.

KU KARANTA: Hanyoyi 5 dake hana furfura fitowa a jikin mutum

Ya caccaki mabiya Sheik Ibrahim Zakzaky a kaikaice inda yace mabiya addini su nisanci tsattsauran ra’ayi da kuma fito na fito da gwamnatin da Allah ya bawa mulki.

Sale Zaria ya kara da cewa akwai banbanci tsakaninsu da kungiyar IMN ta Zakzaky duk da cewa dukkansu yan Shi’a ne.

Idan ka na da wata shawara ko bukatar ba mu labari, a tuntube mu a labaranhausa@corp.legit.ng

Ku same mu a https://www.facebook.com/naijcomhausa Ko a http://twitter.com/naijcomhausa

Latsa wannan domin samun sabuwar manhajar labarai ta Legit.ng Hausa a wayar ku ta hannu: https://play.google.com/store/apps/details?id=com.naij.hausa&hl=en

Asali: Legit.ng

Online view pixel