Dalilin da yasa Yarbawa ba su zabe ni ba a 1999 - Obasanjo

Dalilin da yasa Yarbawa ba su zabe ni ba a 1999 - Obasanjo

Tsohon shugaban kasar Najeriya kuma na farko a wannan jamhuriyar Cif Olusegun Obasanjo ya bayyana dalilin da yake tunanin shine ya sanya 'yan kabilar yarbawa basu zabe sa ba a zaben 1999.

A cewar Cif Obasanjo, yana tunanin saboda ya ki ya shiga kungiyar nan ta hadaddiyar kabilar yarbawan dake kare muradun su ta Afenifere da Marigayi Sanata Abraham Adesanya yake shugabanta a wancan lokacin ne ya janyo hakan.

Dalilin da yasa Yarbawa ba su zabe ni ba a 1999 - Obasanjo
Dalilin da yasa Yarbawa ba su zabe ni ba a 1999 - Obasanjo

KU KARANTA: Buhari ya kama hanyar dawowa gida daga Amurka

Legit.ng ta samu cewa Cif Obasanjo ya ayyana hakan ne a lokacin da yake jawabin sa a lokacin taron shekaru 10 na tunawa da Sanata Abrahim din a birnin Legas.

A wani labarin kuma, Kimanin shekaru 28 da suka shude, Sakataren gwamnatin tarayyar Najeriya Mista Boss Mustapha ya yi bayanin yadda yace tsohon mataimakin shugaban kasar Najeriya Atiku Abubakar ya shirya masa kullalliyar da ta hana shi zama Gwamnan Adamawa.

Kamar dai yadda Boss Mustapha din ya ayyana, biyo bayan sabanin da suka samu da fitaccen dan siyasar Atiku lokacin da ya nemi ya kakaba masa mataimaki, sai kawai ya juya masa baya ya hada kai da jam'iyyar adawa.

Idan ka na da wani shawara ko bukatan bamu labari, tuntube mu a labaranhausa@corp.legit.ng Ku ci gaba da bin mu a Facebook: https://www.facebook.com/naijcomhausa da

Kuma Tuwita: http://twitter.com/naijcomhausa

KU LATSA: Sabuwar hanyar karanta labarain Legit.ng HAUSA

https://play.google.com/store/apps/details?id=com.naij.hausa&hl=en

Asali: Legit.ng

Online view pixel