Angabza kazamin artabu tsakanin 'yan kungiyar OPC da kungiyar asiri

Angabza kazamin artabu tsakanin 'yan kungiyar OPC da kungiyar asiri

Labarin da muke samu na nuni ne da cewa wani babban jami'in 'yan sandan Najeriya mai mukamin Isifecta ya rasa ran sa a sakamakon wani kazamin artabu da ya barke a tsakanin 'yan kungiyar nan na OPC da kuma wata kungiyar asiri a garin Ijebu na jihar Ogun.

Majiyar mu ta tabbatar mana da cewa fadan ya fara ne dai biyo bayan wani tarin gangamin siyasa da Sanata Buruji Kashamu ya gudanar a yankin.

Angabza kazamin artabu tsakanin 'yan kungiyar OPC da kungiyar asiri
Angabza kazamin artabu tsakanin 'yan kungiyar OPC da kungiyar asiri

KU KARANTA: Shugaban INEC ya nuna shakkun sa game da sahihancin zaben 2019

A wani labarin kuma, Babbar jam'iyyar adawa a Najeriya ta People Democratic Party, PDP ta bayyana cewa batun kudurin sake tsayawa takara a zaben 2019 da shugaba Muhammadu Buhari ya ayyana a ranar Litinin din da ta gabata matsalar sa ce da jam'iyyar sa ba ta su ba.

Haka zalika jam'iyyar ta ce har yanzu ita bai ishe ta kallo ba har sai shugaba Buhari din ya samu tikitin takarar a jam'iyyar sa sannan ne za ta maida martani amma ba yanzu ba.

Idan ka na da wani shawara ko bukatan bamu labari, tuntube mu a labaranhausa@corp.legit.ng Ku ci gaba da bin mu a Facebook: https://www.facebook.com/naijcomhausa da

Kuma Tuwita: http://twitter.com/naijcomhausa

KU LATSA: Sabuwar hanyar karanta labarain Legit.ng HAUSA

https://play.google.com/store/apps/details?id=com.naij.hausa&hl=en

Asali: Legit.ng

Online view pixel